< 1 Korintiyawa 14 >

1 Ku dafkaci kauna kuma ku himmatu domin baye bayen ruhaniya, musamman domin kuyi anabci.
Pursue love, and desire the spiritual gifts, but especially that you may prophesy.
2 Domin wanda yake magana da harshe bada mutane yake magana ba amma da Allah. domin babu mai fahimtarsa saboda yana zancen boyayyun abubuwa ciki Ruhu.
Because he who speaks in a ‘language’ is not speaking to people but to God, since no one understands; in spirit he speaks mysteries.
3 Amma wanda yake anabci da mutane yake magana domin ya gina su, ya karfafa su, kuma ya ta'azantar dasu.
But he who prophesies speaks edification and exhortation and comfort to people.
4 Wanda yake magana da wani harshe, kansa yake ginawa, amma mai yin annabci kuwa, ikilisiya yake ginawa.
The one speaking in a ‘language’ edifies himself, but he who prophesies edifies the congregation.
5 To, fatana ace dukan ku kuna magana da harsuna. Amma fiye da hakama, fatana ace kuyi anabci. Wanda yake anabci yafi wanda yake magana da harsuna ( sai dai idan wani ya fassara domin ikilisiya ta ginu).
I could wish that you all spoke in ‘languages’, but even more that you might prophesy; because the one prophesying is greater than the one speaking in ‘languages’ (unless he interprets), so that the congregation may receive edification.
6 Amma yanzu, 'yan'uwa, in na zo wurin ku ina magana da harsuna, ta yaya zaku karu dani? ba zaya yiwu ba, sai idan nayi maku magana da wahayi, ko sani, ko anabci, ko koyarwa.
Now then, brothers, what good will I do you if I come to you speaking in ‘languages’ instead of addressing you with revelation, or with knowledge, or with prophecy, or with teaching?
7 Idan kayan kida marasa rai suna fitar da sauti - kamar su sarewa da algaita - kuma basu fitar da amo daban daban, ta yaya wani zaya san irin amon da sarewar da algaitar suke kadawa?
Take lifeless things like a flute or a harp; if they make no distinction in the notes when they produce sound, how will it be known what is being piped or harped?
8 Domin idan aka busa kaho da sauti marar ma'ana, ta yaya wani zaya san lokacin da ya dace ya shirya zuwa yaki?
Also a trumpet; if it gives an indistinct sound, who will prepare for battle?
9 Haka yake game da ku. Idan kuka furta zance marar ma'ana, ta yaya wani zaya fahimci abinda kukace? zaku yita magana, kuma babu wanda zaya fahimce ku.
So it is with you: if you do not deliver an intelligible message with the ‘language’, how will it be known what is being said? You will just be speaking into the air.
10 Babu shakka akwai harsuna daban daban a duniya, kuma babu wanda baya da ma'ana.
There are probably a great many kinds of sounds in the world, and none of them is without significance.
11 Amma idan ban san ma'anar wani harshe ba, zan zama bare ga mai maganar, kuma mai maganar zaya zama bare a gareni.
But if I do not know the force of the sound, I will be a foreigner to the speaker, and he will be a foreigner to me.
12 haka yake gare ku. Tun da kuna da dokin bayyanuwar Ruhu, ku himmatu da habaka cikin gina ikilisiya.
And you too: since you are zealous for spiritual things, aim at the edification of the congregation, that you may all grow.
13 To wanda yake magana da harshe yayi addu'a domin ya iya fassarawa.
Therefore the one speaking in a ‘language’ should pray that he may interpret.
14 Domin idan nayi addu'a da harshe, ruhuna yayi addu'a, amma fahimtata bata karu ba.
For if I pray in a ‘language’, my spirit prays, but my mind is unfruitful.
15 To, me zan yi? Zan yi addu'a da ruhuna, in kuma yi addu'a da fahimtata. Zan yi raira waka da ruhuna, kuma in raira waka da fahimtata.
So what then? I will pray with the spirit, but I will also pray with the mind; I will sing with the spirit, but I will also sing with the mind.
16 In ba haka ba, idan ka yi yabon Allah da ruhu kawai, ta yaya wanda yake waje zai ce, “Amin” a kan godiyar da kake yi in bai san abin da kake fada ba?
Otherwise, if you bless with the spirit, how will he who occupies the place of the outsider say the “Amen” at your giving of thanks, since he does not know what you are saying?
17 Babu shakka kayi godiya sosai, amma wanin baya ginu ba.
You, of course, give thanks quite well, but the other is not edified.
18 Nagodewa Allah ina magana da harsuna fiye da ku duka.
I thank my God speaking in ‘languages’ more than you all,
19 Duk da haka dai a taron ikilisiya na gwammace in yi magana da kalmomi biyar cikin fahimta saboda inganta wadansu fiye da dubu goma da harshe.
but in the congregation I would rather speak five words with my understanding, precisely so as to instruct others, than ten thousand words in a ‘language’.
20 'Yan'uwa, kada ku zama yara cikin tunani, sai dai a wajen aikin mugunta, ku yi halin jarirai, amma a tunaninku ku girma.
Brothers, stop thinking like children—well, in malice be ‘infants’, but in thinking be adults.
21 A rubuce yake a shari'a cewa, “zan yi magana da mutanen nan ta wurin mutane masu bakin harsuna, da kuma lebunan baki. Duk da haka kuwa ba za su saurare ni ba”, in ji Ubangiji.
In the law it stands written: “I will speak to this people in foreign languages and with different ‘lips’, but not even then will they listen to me,” says the Lord.
22 Amma harsuna alamu ne, ba ga masu bada gaskiya ba, sai dai ga marasa ba da gaskiya. Annabci kuwa alama ce ga masu ba da gaskiya, amma ba don marasa bangaskiya ba.
Therefore the ‘languages’ are for a sign, not to believers but to unbelievers; while prophesying is not for unbelievers but for believers.
23 Saboda haka, in dukan ikilisiya ta taru, kowa kuwa yana magana da wasu harsuna, wadansu na waje da kuma marasa ba da gaskiya suka shigo, ashe, ba sai su ce kun haukace ba ba?
So if the whole congregation comes together and all are speaking in ‘languages’, but outsiders or unbelievers come in, will they not say that you are raving?
24 In kuwa kowa yana yin annabci, wani kuma marar ba da gaskiya ko wani daga waje ya shigo, maganar kuwa zata ratsa shi. Za a ma hukanta shi a kan maganar,
But if everyone is prophesying, and an unbeliever or outsider comes in, he is reproved by all, he is examined by all.
25 asiran zuciyarsa kuma za su tonu. Sakamokon haka, sai ya fadi ya yi wa Allah sujada, zaya furta cewa lallai Allah yana tare da ku.
And thus the secrets of his heart are exposed, and so, falling on his face he will worship God, affirming, “Truly God is among you!”
26 Sai me kuma 'yan'uwa? idan kuka tattaru, wani yana da zabura, koyarwa, wahayi, harshe, ko fassara. Kuyi komai domin gina ikilisiya.
So what goes on, brothers? Whenever you come together, each of you has a psalm, has a teaching, has a ‘language’, has a revelation, has an interpretation. Let all things be done for edification.
27 Idan wani yayi magana da harshe, bari a sami mutum biyu ko uku a yawansu, kuma kowa yayi daya bayan daya. Sai wani ya fassara abinda aka fada.
If anyone speaks in a ‘language’, let it be two—at the most three—and in turn, and let one interpret.
28 Amma idan babu wanda zaya fassara, bari dukansu suyi shiru a ikilisiya. Bari kowa yayi wa kansa maganar a gida shi kadai da kuma Allah.
But if there is no interpreter, let him keep silent in church; let him speak to himself and to God.
29 Bari annabawa biyu ko uku suyi magana, bari sauran su saurara tare da bambance abinda ake fada.
Let two or three prophets speak, and let the others evaluate.
30 Idan kuma anba wani fahimta wanda yana zaune a cikin sujadar, bari wanda yake ta magana kafin yanzu yayi shiru.
But if another who is sitting by receives a revelation, the first should stop speaking.
31 Dukanku kuna iya yin annabci daya bayan daya, domin kowannen ku yayi koyi, a kuma samu karfafawa.
For you can all prophesy one by one, so that all may learn and all may be encouraged.
32 Gama ruhohin annabawa suna karkashin annabawa,
Yes, spirits of prophets are subordinate to prophets.
33 domin Allah ba Allahn rudu ba ne, na salama ne. Haka yake kuwa a duk ikllisiyoyin masu bangaskiya.
Further, God is not a God of disorder but of peace. As in all the congregations of the saints,
34 Mataye suyi shiru a ikilisiyoyi. Domin ba a basu dama ba suyi magana. A maimako, su zama masu sadaukar da kansu, kamar yadda doka ta ce.
your wives should keep silent in the assemblies, for they are not permitted to speak, but to be in subordination, as the law also says.
35 Idan akwai abinda suke so su koya, bari su tambayi mazajen su a gida. Domin abin kunya ne mace tayi magana a ikilisiya.
If they want to learn about something, let them ask their own husbands at home, for it is shameful for women to speak in church.
36 Daga wurinku maganar Allah ta zo ne? ko kuwa a gare ku kadai ta iso?
Or was it from you that the Word of God went forth? Or was it only to you that it came?
37 In wani yana zaton shi ma annabi ne, ko kuwa mai ruhaniya, to, sai ya fahimta, abin nan da nake rubuta maku umarni ne daga wurin Ubangiji.
If anyone thinks that he is a prophet or spiritual, let him acknowledge that the things I write to you are the Lord's commands.
38 In kuwa wani ya ki kula da wannan, shi ma kada a kula da shi.
But if anyone is ignorant, let him remain so.
39 Saboda haka, 'yan'uwa, ku yi marmarin yin annabci sosai, sa'an nan kada ku hana kow yin magana da harsuna.
So then, brothers, seek to prophesy, and do not forbid to speak in ‘languages’.
40 Sai dai a yi komai ta hanyar da ta dace bisa ga tsari.
Let all things be done properly and in order.

< 1 Korintiyawa 14 >