< Zefaniya 1 >

1 Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata. Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
Parole du Seigneur qui fut adressée à Sophonie, fils de Chusi, fils de Godolias, fils d’Amarias, fils d’Ezécias, aux jours de Josias, fils d’Amon, roi de Juda.
2 “Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
Rassemblant je rassemblerai toutes choses de la face de la terre, dit le Seigneur;
3 “Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
Rassemblant les hommes et les bêtes, rassemblant les volatiles du ciel et les poissons de la mer; et la ruine des impies arrivera; et j’exterminerai les hommes de la face de la terre, dit le Seigneur.
4 “Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
Et j’étendrai ma main sur Juda et sur tous les habitants de Jérusalem, et j’exterminerai de ce lieu les restes de Baal, et les noms des gardiens du temple avec les prêtres;
5 waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
Et ceux qui adorent sur les toits la milice du ciel, qui adorent le Seigneur et jurent par lui, et jurent par Melchom;
6 Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
Et ceux qui se détournent en arrière du Seigneur, et ceux qui n’ont pas cherché le Seigneur, et ne s’en sont pas mis en peine.
7 Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
Soyez en silence devant la face du Seigneur Dieu, parce qu’est proche le jour du Seigneur, parce que le Seigneur a préparé une hostie, il a sanctifié ses convives.
8 “A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
Et il arrivera qu’au jour de l’hostie du Seigneur je visiterai les princes et les fils du roi, et ceux qui sont vêtus d’un habit étranger;
9 A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
Et je visiterai quiconque entre arrogamment sur le seuil du temple en ce jour-là, et qui remplit la maison du Seigneur son Dieu d’iniquité et de tromperie.
10 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
Et il y aura, en ce jour-là, dit le Seigneur, une voix de clameur venant de la porte des Poissons, et un hurlement venant de la seconde porte, et le bruit d’une grande ruine venant des collines.
11 Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
Hurlez, habitants de Pila; tout le peuple de Chanaan s’est tu, tous ceux qui étaient couverts d’argent ont été exterminés.
12 A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
Et il arrivera qu’en ce jour je scruterai Jérusalem avec des lampes; et je visiterai les hommes enfoncés dans leur lie; qui disent en leurs cœurs: Le Seigneur ne fera pas de bien, et il ne fera pas de mal.
13 Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
Et leurs richesses seront au pillage, et leurs maisons réduites en un désert; et ils bâtiront des maisons, et ils ne les habiteront pas; et ils planteront des vignes, et ils n’en boiront pas le vin.
14 Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
Il est proche, le grand jour du Seigneur, il est proche et extrêmement prompt; la voix du jour du Seigneur est amère; le fort sera alors dans la tribulation.
15 Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
Jour de colère, ce jour-là; jour de tribulation et d’angoisse; jour de calamité et de misère; jour de ténèbres et d’obscurité, de nuage et de tempête.
16 rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
Jour de la trompe et du bruit retentissant sur les cités fortifiées, et sur les angles élevés.
17 “Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
Et j’affligerai les hommes, et ils marcheront comme des aveugles, parce qu’ils ont péché contre le Seigneur; et leur sang sera répandu comme de la poussière, et leurs corps comme des ordures.
18 Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.
Mais même leur argent et leur or ne pourra les délivrer au jour de la colère du Seigneur; par le feu de son zèle toute la terre sera dévorée, parce qu’il exterminera promptement tous les habitants de la terre.

< Zefaniya 1 >