< Zefaniya 1 >

1 Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
The word of the Lord that came to Sophonias the son of Chusi, the son of Godolias, the son of Amarias, the son of Ezechias, in the days of Josias the son of Amon king of Juda.
2 “Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
Gathering, I will gather together all things from off the face of the land, saith the Lord:
3 “Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
I will gather man, and beast, I will gather the birds of the air, and the fishes of the sea: and the ungodly shall meet with ruin: and I will destroy men from off the face of the land, saith the Lord.
4 “Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
And I will stretch out my hand upon Juda, and upon all the inhabitants of Jerusalem: and I will destroy out of this place the remnant of Baal, and the names of the wardens of the temples with the priests:
5 waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
And them that worship the host of heaven upon the tops of houses, and them that adore, and swear by the Lord, and swear by Melchom.
6 Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
And them that turn away from following after the Lord, and that have not sought the Lord, nor searched after him.
7 Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
Be silent before the face of the Lord God: for the day of the Lord is near, for the Lord hath prepared a victim, he hath sanctified his guests.
8 “A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
And it shall come to pass in the day of the victim of the Lord, that I will visit upon the princes, and upon the king’s sons, and upon all such as are clothed with strange apparel.
9 A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
And I will visit in that day upon every one that entereth arrogantly over the threshold: them that fill the house of the Lord their God with iniquity and deceit.
10 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
And there shall be in that day, saith the Lord, the noise of a cry from the fish gate, and a howling from the Second, and a great destruction from the hills.
11 Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
Howl, ye inhabitants of the Morter. All the people of Chanaan is hush, all are cut off that were wrapped up in silver.
12 A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
And it shall come to pass at that time, that I will search Jerusalem with lamps, and will visit upon the men that are settled on their lees: that say in their hearts: The Lord will not do good, nor will he do evil.
13 Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
And their strength shall become a booty, and their houses as a desert: and they shall build houses, and shall not dwell in them: and they shall plant vineyards, and shall not drink the wine of them.
14 Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
The great day of the Lord is near, it is near and exceeding swift: the voice of the day of the Lord is bitter, the mighty man shall there meet with tribulation.
15 Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
That day is a day of wrath, a day of tribulation and distress, a day of calamity and misery, a day of darkness and obscurity, a day of clouds and whirlwinds,
16 rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
A day of the trumpet and alarm against the fenced cities, and against the high bulwarks.
17 “Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
And I will distress men, and they shall walk like blind men, because they have sinned against the Lord: and their blood shall be poured out as earth, and their bodies as dung.
18 Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.
Neither shall their silver and their gold be able to deliver them in the day of the wrath of the Lord: all the land shall be devoured by the fire of his jealousy, for he shall make even a speedy destruction of all them that dwell in the land.

< Zefaniya 1 >