< Zefaniya 2 >
1 Ku tattaru, ku tattaru, Ya ku al’umma marar kunya,
Be ashamed within yourselves, be ashamed,
2 kafin ƙayyadadden lokacin nan yă zo ranan nan kuma ta share ku kamar ƙaiƙayi kuma kafin fushi mai tsanani na Ubangiji yă auko muku, kafin ranar fushin Ubangiji ta auko muku.
before you become as the drifting chaff, before the anger of the Lord comes upon you, before the day of the Lord’s wrath comes upon you.
3 Ku nemi Ubangiji, dukanku ƙasashe masu tawali’u, ku da kuke yin abin da ya umarta. Ku nemi adalci da tawali’u; mai yiwuwa ku sami mafaka a ranar fushin Ubangiji.
Seek the Lord all you meek of the earth, you who obey his law; Seek righteousness, seek meekness; perhaps you may be hidden in the day of the Lord’s wrath.
4 Za a yashe Gaza a kuma bar Ashkelon kango. Da tsakar rana Ashdod za tă zama babu kowa a kuma tumɓuke Ekron.
For Gaza will be forsaken; Ashkelon a desolation; Ashdod – by noon will they rout her and Ekron be torn up!
5 Taku ta ƙare ku da kuke zama a bakin teku, Ya ku mutanen Keretawa; maganar Ubangiji tana gāba da ke, Ya ke Kan’ana, ƙasar Filistiyawa. “Zan hallaka ki kuma babu abin da zai rage.”
Woe to those who live by the sea coast, people of the Cherethites! The word of the Lord is against you, Canaan, land of the Philistines! I will destroy you so that you will be without inhabitants,
6 Ƙasar da take a bakin teku, inda Keretawa suke zaune, za tă zama wurin da makiyaya da ta garken tumaki.
and you will become shepherds’ cots and folds for flocks.
7 Za tă zama mallakar raguwar gidan Yahuda; a can za su sami wurin kiwo. Da yamma za su kwanta a gidajen Ashkelon. Ubangiji Allahnsu zai lura da su; zai maido musu da martabarsu.
The sea coast will belong to the survivors of the house of Judah. They will pasture their flocks there. In the house of Ashkelon they will lie down at evening. The Lord their God will be with them and restore their fortunes.
8 “Na ji irin zagin da Mowab take yi, da kuma ba’ar Ammonawa, waɗanda suka zagi mutanena suna kuma yi barazana a kan ƙasarsu.
I have heard the taunts of Moab, and the revilings of the Ammonites, how they have taunted my people, and spoken boastfully concerning their border.
9 Saboda haka, muddin ina raye,” in ji Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, “tabbatacce Mowab za tă zama kamar Sodom, Ammonawa kuma kamar Gomorra, ƙasa mai ciyayi da rammukan gishiri, ƙasa marar amfani har abada. Raguwar mutanena za su washe su; waɗanda suka rage na al’ummata za su gāda ƙasarsu.”
Therefore as I live, says the Lord of hosts, the God of Israel: Moab will be like Sodom, and the Ammonites like Gomorrah, a pile of nettles and saltpits, and a desolation, forever. The residue of my people will plunder them, and the survivors of my nation will inherit them.
10 Wannan ne zai zama sakamakon girmankansu, saboda zagi da kuma ba’ar da suka yi wa mutanen Ubangiji Maɗaukaki.
This will they have for their pride, because they have taunted and spoken boastfully against the people of the Lord of hosts.
11 Ubangiji zai zama abin tsoro a gare su sa’ad da ya hallaka allolin ƙasar. Al’ummai a kowane bakin teku za su yi masa sujada, kowa a ƙasarsa.
The Lord will terrify them; he will reduce all the gods of the earth; then all the peoples of the nations will worship him, each in their own land.
12 “Ku ma, ya Kushawa, za a kashe ku da takobina.”
You, also, Ethiopians, slain by his sword are you!
13 Zai kuma miƙa hannunsa gāba da arewa yă kuma hallaka Assuriya, zai mai da Ninebe kango gaba ɗaya ta kuma zama busasshiya kamar hamada.
And he will stretch out his hand against the north and destroy Assyria; And he will make Nineveh a desolation, dry as the wilderness.
14 Garkuna za su kwanta a can, da kowace irin halitta, Mujiyar hamada da bushiya za su zauna a kan ginshiƙanta. Kukansu za tă ratsa tagogi, ɓuraguzai za su tare ƙofofin shiga, za a kware ginshiƙan al’ul.
Herds will lie down in it, every beast of the earth, Desert owl and screech owl will lodge in its capitals. The owl will hoot in the window, the raven on the doorstep, all stripped bare of cedar.
15 Birnin da yake harka ke nan da take zaune lafiya. Ta ce wa kanta, “Ni ce, kuma babu kamata.” Dubi irin kangon da ta zama mana, mazaunin namun jeji! Duk wanda ya wuce ta sai ya yi mata tsaki yana kaɗa kai.
This is the exultant city which sat secure. The city who said to herself, I am and there is none else! How has she become a desolation! A lair of beasts! Every passerby hisses at her, shakes their hand.