< Zefaniya 2 >
1 Ku tattaru, ku tattaru, Ya ku al’umma marar kunya,
Search yourselves; yea, search, O nation without shame!
2 kafin ƙayyadadden lokacin nan yă zo ranan nan kuma ta share ku kamar ƙaiƙayi kuma kafin fushi mai tsanani na Ubangiji yă auko muku, kafin ranar fushin Ubangiji ta auko muku.
Before the decree bring forth, Before the day come upon you like chaff; Before the fierce anger of Jehovah come upon you, Before the day of the anger of Jehovah come upon you.
3 Ku nemi Ubangiji, dukanku ƙasashe masu tawali’u, ku da kuke yin abin da ya umarta. Ku nemi adalci da tawali’u; mai yiwuwa ku sami mafaka a ranar fushin Ubangiji.
Seek ye Jehovah, all ye lowly of the land, Ye, who obey his commands! Seek righteousness; seek lowliness; It may be that ye shall be hid in the day of the anger of Jehovah.
4 Za a yashe Gaza a kuma bar Ashkelon kango. Da tsakar rana Ashdod za tă zama babu kowa a kuma tumɓuke Ekron.
For Gaza shall be forsaken, And Askelon a desolation; Ashdod shall be driven out at noonday, And Ekron shall be rooted up.
5 Taku ta ƙare ku da kuke zama a bakin teku, Ya ku mutanen Keretawa; maganar Ubangiji tana gāba da ke, Ya ke Kan’ana, ƙasar Filistiyawa. “Zan hallaka ki kuma babu abin da zai rage.”
Woe to the inhabitants of the sea-coasts, the nation of the Cherethites! This is the word of Jehovah against you, O Canaan, land of the Philistines: “I will destroy thee, that there shall be no inhabitant.”
6 Ƙasar da take a bakin teku, inda Keretawa suke zaune, za tă zama wurin da makiyaya da ta garken tumaki.
And the sea-coast shall be pastures full of habitations for shepherds, and folds for flocks.
7 Za tă zama mallakar raguwar gidan Yahuda; a can za su sami wurin kiwo. Da yamma za su kwanta a gidajen Ashkelon. Ubangiji Allahnsu zai lura da su; zai maido musu da martabarsu.
The coast shall be for the residue of the house of Judah; Thereon shall they feed; In the houses of Askelon shall they lie down in the evening; For Jehovah their God will look upon them, and bring back their captives.
8 “Na ji irin zagin da Mowab take yi, da kuma ba’ar Ammonawa, waɗanda suka zagi mutanena suna kuma yi barazana a kan ƙasarsu.
I have heard the reproach of Moab, And the revilings of the sons of Ammon, With which they have reproached my people, And exalted themselves against their borders.
9 Saboda haka, muddin ina raye,” in ji Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, “tabbatacce Mowab za tă zama kamar Sodom, Ammonawa kuma kamar Gomorra, ƙasa mai ciyayi da rammukan gishiri, ƙasa marar amfani har abada. Raguwar mutanena za su washe su; waɗanda suka rage na al’ummata za su gāda ƙasarsu.”
Therefore, as I live, saith Jehovah of hosts, the God of Israel, Moab shall be as Sodom, And the sons of Ammon as Gomorrah, A possession for thorns, and a pit for salt, and a perpetual desolation. The residue of my people shall spoil them, And the remainder of my nation shall possess them.
10 Wannan ne zai zama sakamakon girmankansu, saboda zagi da kuma ba’ar da suka yi wa mutanen Ubangiji Maɗaukaki.
This shall come upon them for their pride, Because they have uttered reproaches, and exalted themselves against the people of Jehovah of hosts.
11 Ubangiji zai zama abin tsoro a gare su sa’ad da ya hallaka allolin ƙasar. Al’ummai a kowane bakin teku za su yi masa sujada, kowa a ƙasarsa.
Jehovah will be terrible against them; For he will destroy all the gods of the earth; And before him shall worship, every one from his place, All the islands of the nations.
12 “Ku ma, ya Kushawa, za a kashe ku da takobina.”
Ye, also, O Ethiopians! Ye shall be slain by my sword!
13 Zai kuma miƙa hannunsa gāba da arewa yă kuma hallaka Assuriya, zai mai da Ninebe kango gaba ɗaya ta kuma zama busasshiya kamar hamada.
He will also stretch out his hand against the North, And destroy Assyria, And make Nineveh a desolation, Even dry like a desert.
14 Garkuna za su kwanta a can, da kowace irin halitta, Mujiyar hamada da bushiya za su zauna a kan ginshiƙanta. Kukansu za tă ratsa tagogi, ɓuraguzai za su tare ƙofofin shiga, za a kware ginshiƙan al’ul.
And flocks shall lie down in the midst of her, Yea, all the tribes of wild beasts; The pelican and the hedgehog shall lodge in the capitals of her pillars; A cry shall resound in the window; Desolation shall be upon the threshold; For her cedar-work shall be laid bare.
15 Birnin da yake harka ke nan da take zaune lafiya. Ta ce wa kanta, “Ni ce, kuma babu kamata.” Dubi irin kangon da ta zama mana, mazaunin namun jeji! Duk wanda ya wuce ta sai ya yi mata tsaki yana kaɗa kai.
This is the rejoicing city that dwelt in security, That said in her heart, “I, and none besides me!” Now is she become a desolation, a resting-place for wild beasts! Every one that passeth by her shall hiss, and wag his hand.