< Zefaniya 1 >

1 Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata. Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
Este es el mensaje que el Señor le dio a Sofonías. Él era el hijo de Cusí, hijo de Guedalías, hijo de Amarías, hijo de Ezequías. Esto pasó cuando Josías, hijo de Amón, era rey de Judá.
2 “Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
Yo destruiré por complete todo de la faz de la tierra, declara el Señor.
3 “Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
Yo destruiré a toda persona y animal, destruiré a las aves del vielo, y los peces del mar. Acabaré con los malvados, y destruiré a la raza humana de la faz de la tierra.
4 “Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
Golpearé a Judá y a todos los que viven en Jerusalén. Además destruiré todo lo que queda de su culto a Baal, junto con sus sacerdotes paganos para que hasta sus nombres sean olvidados.
5 waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
Destruiré también a los que suben a las azoteas para inclinarse ante el sol, la luna y las estrellas. Ellos también se inclinan y juran fidelidad al Señor, pero lo mismo hacen con Milcón.
6 Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
Destruiré a os que una vez adoraron al Señor y dejaron de hacerlo. Ellos no buscan al Señor ni piden mi ayuda.
7 Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
¡Callen ante el Señor Dios! Porque el día del Señor está cerca: el Señor ha preparado un sacrificio consagrado a sus invitados.
8 “A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
Entonces, en el día del sacrificio del Señor yo castigaré a los oficiales y a los hijos del rey, y a los que siguen los caminos paganos.
9 A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
También castigaré a los que saltan por encima del umbral. Ese día castigaré a los que llenan las casa de sus amos con violencia y engaño.
10 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
Ese día, declara el Señor, un grito de lamento saldrá de la Puerta del Pez, un lamento saldrá del Segundo Barrio, y un fuerte estrépito de las montañas.
11 Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
Los que viven en el Barrio del Mercado se lamentarán porque los mercaderes estarán destruidos, así como los que comercian la plata.
12 A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
En ese tiempo, buscaré por toda Jerusalén con lámparas y castigaré a los jactanciosos, que son como los residuos de vino podrido, y que dicen para sí mismos: “El Señor no hará bien ni mal”.
13 Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
Sus posesiones serán saqueadas y sus casas quedarán destruidas. Construirán casas pero no vivirán en ellas. Plantarán viñedos, pero no beberán el vino.
14 Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
El gran día del Señor está cerca y se aproxima con prontitud. Será un día amargo, e incluso los guerreros clamarán en voz alta.
15 Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
Será un día de enojo, un día de tribulación y angustia; un día de ruina y desastre; un día de oscuridad y penumbra, un día aciago con nubes negras;
16 rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
un día de sonido de trompetas y gritos de guerra contra ciudades fortificadas y torres de vigilancia.
17 “Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
Traeré angustia sobre la humanidad, haciéndolos caminar como ciegos porque han pecado contra el Señor. Su sangre se derramará como una gran cantidad de polvo, y sus intestinos como el excremento.
18 Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.
Su plata y su oro no los salvarán el día de la ira del Señor. Toda la tierra será consumida con el fuego del celo de su ira. Él se asegurará de que la destrucción de los habitantes del mundo sea repentina y completa.

< Zefaniya 1 >