< Zefaniya 1 >
1 Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
Parole de Yahvé qui fut adressée à Sophonie, fils de Cushi, fils de Guedalia, fils d'Amaria, fils d'Ézéchias, du temps de Josias, fils d'Amon, roi de Juda.
2 “Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
Je vais tout balayer de la surface de la terre, dit Yahvé.
3 “Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
Je balaierai l'homme et l'animal. Je balaierai les oiseaux du ciel, les poissons de la mer, et les tas de décombres avec les méchants. J'exterminerai l'homme de la surface de la terre, dit Yahvé.
4 “Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
J'étendrai ma main contre Juda et contre tous les habitants de Jérusalem. J'exterminerai de ce lieu le reste de Baal, le nom des prêtres idolâtres et païens,
5 waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
ceux qui adorent l'armée du ciel sur les toits, ceux qui adorent et jurent par Yahvé et qui jurent aussi par Malcom,
6 Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
ceux qui se sont détournés de Yahvé, ceux qui n'ont pas cherché Yahvé et ne l'ont pas recherché.
7 Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
Taisez-vous devant le Seigneur Yahvé, car le jour de Yahvé est proche. Car Yahvé a préparé un sacrifice. Il a consacré ses hôtes.
8 “A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
Au jour du sacrifice de l'Éternel, je punirai les princes, les fils du roi et tous ceux qui sont revêtus de vêtements étrangers.
9 A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
En ce jour-là, je punirai tous ceux qui sautent par-dessus le seuil, qui remplissent la maison de leur maître par la violence et la tromperie.
10 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
En ce jour-là, dit l'Éternel, il y aura un cri de la porte des poissons, un gémissement du deuxième quartier, et un grand fracas des collines.
11 Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
Gémissez, habitants de Maktesh, car tout le peuple de Canaan est perdu! Tous ceux qui étaient chargés d'argent sont exterminés.
12 A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
En ce temps-là, je fouillerai Jérusalem avec des lampes, et je punirai les hommes installés sur leur lie, qui disent en leur cœur: « L'Éternel ne fera pas le bien, il ne fera pas le mal. »
13 Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
Leurs richesses deviendront un butin, et leurs maisons une désolation. Oui, ils construiront des maisons, mais ils ne les habiteront pas. Ils planteront des vignes, mais ils ne boiront pas leur vin.
14 Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
Le grand jour de Yahvé est proche. Elle est proche et se précipite, la voix du jour de Yahvé. Le puissant y pousse des cris amers.
15 Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
Ce jour-là est un jour de colère, un jour de détresse et d'angoisse, un jour de trouble et de ruine, un jour de ténèbres et d'obscurité, un jour de nuages et d'obscurité,
16 rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
un jour de trompette et d'alarme contre les villes fortes et contre les hauts remparts.
17 “Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
Je ferai venir sur les hommes une telle détresse qu'ils marcheront comme des aveugles, parce qu'ils auront péché contre Yahvé. Leur sang sera répandu comme de la poussière et leur chair comme du fumier.
18 Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.
Ni leur argent, ni leur or ne pourront les délivrer au jour de la colère de l'Éternel, mais tout le pays sera dévoré par le feu de sa jalousie, car il fera périr, terriblement périr, tous les habitants du pays.