< Zakariya 1 >

1 A wata na bakwai na shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
In the eighth month, in the second year of Darius, came the word of the Lord unto Zechariah, the son of Berechyah, the son of 'Iddo the prophet, saying,
2 “Ubangiji ya yi fushi sosai da kakanninku.
The Lord hath been greatly angry with your fathers.
3 Saboda haka ka gaya wa mutanen, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku komo gare ni,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘ni kuma zan komo gare ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And [now] say thou unto them, Thus hath said the Lord of hosts, Return ye unto me, saith the Lord of hosts, and I will return unto you: so hath said the Lord of hosts.
4 Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka ce musu, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku juya daga mugayen hanyoyinku da mugayen abubuwan da kuke yi.’ Amma ba su saurara ba, ko ma su kula da ni, in ji Ubangiji.
Be ye not like your fathers, unto whom the former prophets proclaimed, saying, Thus hath said the Lord of hosts, Do return from your evil ways, and your evil doings; but they did not hear, nor listen unto me, saith the Lord.
5 Yanzu ina kakanninku suke? Annabawan kuma fa, sun rayu har abada ne?
Your fathers, —where are they! and the prophets, — could they live for ever!
6 Amma maganata da dokokina da na umarta ta wurin bayina annabawa fa, ashe, ba su tabbata ba a kan kakanninku? “Sa’an nan suka tuba suka ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki ya yi mana daidai abin da hanyoyinmu suka cancanci mu samu, kamar dai yadda ya yi niyya yi.’”
But my words and my decrees, which I commanded my servants the prophets, behold, they did overtake your fathers: and [then] they returned and said, Just as the Lord of hosts had purposed to do unto us, in accordance with our ways, and in accordance with our doings, so hath he dealt with us.
7 A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato, watan Shebat, a shekara ta biyu ta Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
On the four and twentieth day of the eleventh month, which is the month of Shebat, in the second year of Darius, came the word of the Lord unto Zechariah, the son of Berechyahu, the son of 'Iddo the prophet, saying,
8 Da dare, na ga wahayi, a gabana kuwa ga mutum a kan jan doki! Yana tsaye a cikin itatuwa masu furanni, a bayansa a cikin itatuwan ci-zaƙi, a bayansa kuwa akwai dawakai masu ruwan ja, ruwan ƙasa-ƙasa da kuma ruwan fari.
I saw this night, and behold there was a man riding upon a red horse, and he was standing among the myrtle-trees that were in the deep valley; and behind him were red, pale, and white horses.
9 Sai na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan ranka yă daɗe?” Mala’ikan da yake magana da ni ya amsa ya ce, “Zan nuna maka mene ne su.”
And I said, What are these, O my lord? Then said unto me the angel that spoke with me, I will show thee what these are.
10 Sai mutumin da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin ya yi bayani cewa, “Su ne waɗanda Ubangiji ya aika ko’ina a duniya.”
And the man that stood among the myrtle-trees answered and said, These are those whom the Lord hath sent to traverse the earth.
11 Sai suka ce wa mala’ikan da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun ratsa ko’ina a duniya, sai muka ga duniya duka tana zaman lafiya.”
And they answered the angel of the Lord that stood among the myrtle-trees, and said, We have traversed the earth, and, behold, all the earth is inhabited quietly, and is at rest.
12 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
Then commenced the angel of the Lord, and said, O Lord of hosts, how long yet wilt thou not have mercy on Jerusalem and on the cities of Judah, against which thou hast been indignant these seventy years?
13 Sai Ubangiji ya yi wa mala’ikan da ya yi magana da ni magana da kalmomi masu daɗi da kuma masu ta’azantarwa.
And the Lord answered the angel that spoke with me with good words and comforting words.
14 Sai mala’ikan da yake magana da ni ya ce, “Ka yi shelar maganan nan, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ina kishi domin Urushalima da Sihiyona,
And the angel that spoke with me said unto me, Proclaim thou, saying, Thus hath said the Lord of hosts, I am jealous for Jerusalem and for Zion with a great jealousy.
15 amma ina fushi da ƙasashen da suke ji suna zaman lafiya, na ɗan yi fushina kawai, amma sai suka ƙara musu masifar.’
And with a great anger will I be angry with the nations that are at ease; for I was but a little angry [with Zion], and they helped forward the mischief.
16 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Zan komo Urushalima da jinƙai, a can ne za a sāke gina gidana. Za a kuma miƙe ma’auni a bisa Urushalima,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Therefore thus hath said the Lord, I am returned to Jerusalem in mercy: my house shall be rebuilt in it, saith the Lord of hosts, and the measuring-line shall be stretched forth over Jerusalem.
17 “Ci gaba da yin shela, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Garuruwana za su sāke kwarara da wadata, Ubangiji kuma zai sāke yi wa Sihiyona ta’aziyya, yă kuma zaɓi Urushalima.’”
Proclaim yet [farther], saying, Thus hath said the Lord of hosts, My cities shall again overflow with prosperity: and the Lord will again comfort Zion, and make choice again of Jerusalem.
18 Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
And I lifted up my eyes, and saw, and behold, there were four horns.
19 Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
And I said unto the angel who spoke with me, What are these? And he said unto me, These are the horns that have dispersed Judah, Israel, and Jerusalem.
20 Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
And the Lord showed me four carpenters.
21 Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”
Then said I, What are these coming to do? And he said as followeth, These are the horns that have dispersed Judah, to the extent that no man could lift up his head; but these are come to terrify them, to cast off the horns of the nations, that have been lifting up their horn over the land of Judah to disperse it.

< Zakariya 1 >