< Zakariya 1 >

1 A wata na bakwai na shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
In the eighth month, in the second year of king Darius, the word of the Lord came to Zacharias the son of Barachias, the son of Addo, the prophet, saying:
2 “Ubangiji ya yi fushi sosai da kakanninku.
The Lord hath been exceeding angry with your fathers.
3 Saboda haka ka gaya wa mutanen, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku komo gare ni,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘ni kuma zan komo gare ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And thou shalt say to them: Thus saith the Lord of hosts: Turn ye to me, saith the Lord of hosts: and I will turn to you, saith the Lord of hosts.
4 Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka ce musu, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku juya daga mugayen hanyoyinku da mugayen abubuwan da kuke yi.’ Amma ba su saurara ba, ko ma su kula da ni, in ji Ubangiji.
Be not as your fathers, to whom the former prophets have cried, saying: Thus saith the Lord of hosts: Turn ye from your evil ways, and from your wicked thoughts: but they did not give ear, neither did they hearken to me, saith the Lord.
5 Yanzu ina kakanninku suke? Annabawan kuma fa, sun rayu har abada ne?
Your fathers, where are they? and the prophets, shall they live always?
6 Amma maganata da dokokina da na umarta ta wurin bayina annabawa fa, ashe, ba su tabbata ba a kan kakanninku? “Sa’an nan suka tuba suka ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki ya yi mana daidai abin da hanyoyinmu suka cancanci mu samu, kamar dai yadda ya yi niyya yi.’”
But yet my words, and my ordinances, which I gave in charge to my servants the prophets, did they not take hold of your fathers, and they returned, and said: As the Lord of hosts thought to do to us according to our ways, and according to our devices, so he hath done to us.
7 A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato, watan Shebat, a shekara ta biyu ta Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
In the four and twentieth day of the eleventh month which is called Sabath, in the second year of Darius, the word of the Lord came to Zacharias the son of Barachias, the son of Addo, the prophet, saying:
8 Da dare, na ga wahayi, a gabana kuwa ga mutum a kan jan doki! Yana tsaye a cikin itatuwa masu furanni, a bayansa a cikin itatuwan ci-zaƙi, a bayansa kuwa akwai dawakai masu ruwan ja, ruwan ƙasa-ƙasa da kuma ruwan fari.
I saw by night, and behold a man riding upon a red horse, and he stood among the myrtle trees, that were in the bottom: and behind him were horses, red, speckled, and white.
9 Sai na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan ranka yă daɗe?” Mala’ikan da yake magana da ni ya amsa ya ce, “Zan nuna maka mene ne su.”
And I said: What are these, my Lord? and the angel that spoke in me, said to me: I will shew thee what these are:
10 Sai mutumin da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin ya yi bayani cewa, “Su ne waɗanda Ubangiji ya aika ko’ina a duniya.”
And the man that stood among the myrtle trees answered, and said: These are they, whom the Lord hath sent to walk through the earth.
11 Sai suka ce wa mala’ikan da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun ratsa ko’ina a duniya, sai muka ga duniya duka tana zaman lafiya.”
And they answered the angel of the Lord, that stood among the myrtle trees, and said: We have walked through the earth, and behold all the earth is inhabited, and is at rest.
12 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
And the angel of the Lord answered, and said: O Lord of hosts, how long wilt thou not have mercy on Jerusalem, and on the cities of Juda, with which thou hast been angry? this is now the seventieth year.
13 Sai Ubangiji ya yi wa mala’ikan da ya yi magana da ni magana da kalmomi masu daɗi da kuma masu ta’azantarwa.
And the Lord answered the angel, that spoke in me, good words, comfortable words.
14 Sai mala’ikan da yake magana da ni ya ce, “Ka yi shelar maganan nan, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ina kishi domin Urushalima da Sihiyona,
And the angel that spoke in me, said to me: Cry thou, saying: Thus saith the Lord of hosts: I am zealous for Jerusalem, and Sion with a great zeal.
15 amma ina fushi da ƙasashen da suke ji suna zaman lafiya, na ɗan yi fushina kawai, amma sai suka ƙara musu masifar.’
And I am angry with a great anger with the wealthy nations: for I was angry a little, but they helped forward the evil.
16 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Zan komo Urushalima da jinƙai, a can ne za a sāke gina gidana. Za a kuma miƙe ma’auni a bisa Urushalima,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Therefore thus saith the Lord: I will return to Jerusalem in mercies: my house shall be built in it, saith the Lord of hosts: and the building line shall be stretched forth upon Jerusalem.
17 “Ci gaba da yin shela, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Garuruwana za su sāke kwarara da wadata, Ubangiji kuma zai sāke yi wa Sihiyona ta’aziyya, yă kuma zaɓi Urushalima.’”
Cry yet, saying: Thus saith the Lord of hosts: My cities shall yet flow with good things: and the Lord will yet comfort Sion, and he will yet choose Jerusalem.
18 Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
And I lifted up my eyes, and saw: and behold four horns.
19 Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
And I said to the angel that spoke to me: What are these? And he said to me: These are the horns that have scattered Juda, and Israel, and Jerusalem.
20 Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
And the Lord shewed me four smiths.
21 Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”
And I said: What come these to do? and he spoke, saying: These are the horns which have scattered Juda every man apart, and none of them lifted up his head: and these are come to fray them, to cast down the horns of the nations, that have lifted up the horn upon the land of Juda to scatter it.

< Zakariya 1 >