< Zakariya 1 >

1 A wata na bakwai na shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
Měsíce osmého, léta druhého Dariova, stalo se slovo Hospodinovo k Zachariášovi synu Barachiáše, syna Iddova, proroku, řkoucí:
2 “Ubangiji ya yi fushi sosai da kakanninku.
Rozhněval se Hospodin na otce vaše velice.
3 Saboda haka ka gaya wa mutanen, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku komo gare ni,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘ni kuma zan komo gare ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Protož rci těmto: Takto praví Hospodin zástupů: Navraťte se ke mně, praví Hospodin zástupů, a navrátím se k vám, praví Hospodin zástupů.
4 Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka ce musu, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku juya daga mugayen hanyoyinku da mugayen abubuwan da kuke yi.’ Amma ba su saurara ba, ko ma su kula da ni, in ji Ubangiji.
Nebuďte jako otcové vaši, na něž volávali proroci onino předešlí, říkajíce: Takto praví Hospodin zástupů: Navraťte se nyní od cest svých zlých, i od skutků vašich zlých, ale neuposlechli, ani pozorovali mne, praví Hospodin.
5 Yanzu ina kakanninku suke? Annabawan kuma fa, sun rayu har abada ne?
Otcové vaši kde jsou? A proroci ti zdali na věky živi jsou?
6 Amma maganata da dokokina da na umarta ta wurin bayina annabawa fa, ashe, ba su tabbata ba a kan kakanninku? “Sa’an nan suka tuba suka ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki ya yi mana daidai abin da hanyoyinmu suka cancanci mu samu, kamar dai yadda ya yi niyya yi.’”
Ale však slova má a soudové moji, kteréž jsem přikázal služebníkům svým prorokům, zdali nepostihli otců vašich? tak že obrátivše se, řekli: Jakž uložil Hospodin zástupů učiniti nám podlé cest našich, a podlé skutků našich, tak učinil nám.
7 A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato, watan Shebat, a shekara ta biyu ta Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
Dne čtyřmecítmého, jedenáctého měsíce, kterýž jest měsíc Šebat, léta druhého Dariova, stalo se slovo Hospodinovo k Zachariášovi synu Barachiáše, syna Iddova, proroku, řkoucí:
8 Da dare, na ga wahayi, a gabana kuwa ga mutum a kan jan doki! Yana tsaye a cikin itatuwa masu furanni, a bayansa a cikin itatuwan ci-zaƙi, a bayansa kuwa akwai dawakai masu ruwan ja, ruwan ƙasa-ƙasa da kuma ruwan fari.
Viděl jsem v noci, a aj, muž sedí na koni ryzím, kterýž stál mezi myrtovím, kteréž bylo v dolině, za ním pak koně ryzí, strakaté a bílé.
9 Sai na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan ranka yă daɗe?” Mala’ikan da yake magana da ni ya amsa ya ce, “Zan nuna maka mene ne su.”
I řekl jsem: Kdo jsou tito, Pane můj? Řekl mi anděl ten, kterýž mluvil se mnou: Já ukáži tobě, kdo jsou tito.
10 Sai mutumin da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin ya yi bayani cewa, “Su ne waɗanda Ubangiji ya aika ko’ina a duniya.”
Tedy odpovídaje muž ten, kterýž stál mezi myrtovím, řekl: Tito jsou, kteréž poslal Hospodin, aby zchodili zemi.
11 Sai suka ce wa mala’ikan da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun ratsa ko’ina a duniya, sai muka ga duniya duka tana zaman lafiya.”
I odpověděli andělu Hospodinovu tomu, kterýž stál mezi myrtovím, a řekli: Zchodili jsme zemi, a aj, všecka země bezpečně bydlí, a pokoje užívá.
12 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
Tedy odpověděl anděl Hospodinův a řekl: Ó Hospodine zástupů, až dokudž ty se nesmiluješ nad Jeruzalémem a nad městy Judskými, na kteréž jsi hněval se již sedmdesáte let?
13 Sai Ubangiji ya yi wa mala’ikan da ya yi magana da ni magana da kalmomi masu daɗi da kuma masu ta’azantarwa.
I odpověděl Hospodin andělu tomu, kterýž mluvil se mnou, slovy dobrými, slovy potěšitelnými.
14 Sai mala’ikan da yake magana da ni ya ce, “Ka yi shelar maganan nan, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ina kishi domin Urushalima da Sihiyona,
Tedy řekl mi anděl, kterýž mluvil ke mně: Volej a rci: Takto praví Hospodin zástupů: Horlím pro Jeruzalém a Sion horlením velikým.
15 amma ina fushi da ƙasashen da suke ji suna zaman lafiya, na ɗan yi fushina kawai, amma sai suka ƙara musu masifar.’
A hněvám se náramně na ty národy, kteříž mají pokoj; nebo když jsem já se málo rozhněval, oni pomáhali k zlému.
16 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Zan komo Urushalima da jinƙai, a can ne za a sāke gina gidana. Za a kuma miƙe ma’auni a bisa Urushalima,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Protož takto praví Hospodin: Navrátil jsem se k Jeruzalému milosrdenstvím, dům můj staven bude v něm, praví Hospodin zástupů, a pravidlo vztaženo bude na Jeruzalém.
17 “Ci gaba da yin shela, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Garuruwana za su sāke kwarara da wadata, Ubangiji kuma zai sāke yi wa Sihiyona ta’aziyya, yă kuma zaɓi Urushalima.’”
Ještě volej a rci: Takto praví Hospodin zástupů: Ještěť se rozsadí města má pro hojnost dobrého; neboť utěší ještě Hospodin Sion, a vyvolí ještě Jeruzalém.
18 Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
Tedy pozdvihl jsem očí svých, a uzřel jsem, a aj, čtyři rohové.
19 Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
I řekl jsem andělu, kterýž mluvil se mnou: Co jest toto? I řekl mi: To jsou ti rohové, kteříž zmítali Judou, Izraelem a Jeruzalémem.
20 Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
Ukázal mi také Hospodin čtyři kováře.
21 Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”
I řekl jsem: Co jdou dělati tito? I mluvil, řka: Tito jsou rohové, kteříž zmítali Judou, tak že žádný nemohl pozdvihnouti hlavy své. Protož přišli tito, aby je přestrašili, a srazili rohy těch národů, kteříž pozdvihli rohu proti zemi Judské, aby ní zmítali.

< Zakariya 1 >