< Zakariya 9 >
1 Annabci. Maganar Ubangiji tana gāba da ƙasar Hadrak za tă kuma sauko a kan Damaskus, gama idanun dukan mutane da na kabilan Isra’ila suna a kan Ubangiji,
Пророчество словесе Господня в земли Седраха и Дамаска жертвы его: зане Господь призирает на человеки и на вся колена Израилева,
2 da kuma a kan Hamat ita ma, wadda ta yi iyaka da ita, da kuma a kan Taya da Sidon, ko da yake suna da hikima ƙwarai.
и во Имафе в пределех его Тир и Сидон, яко умудреша зело.
3 Taya ta gina wa kanta mafaka mai ƙarfi; ta tara azurfa kamar ƙasa, zinariya kuma kamar tarin shara a tituna.
И созда Тир твердыни себе и собра сребро яко персть и злато яко брение путий.
4 Amma Ubangiji zai karɓe mallakarta, zai hallaka ikonta da take da shi a kan teku, wuta kuma za tă cinye ta.
Сего ради Господь наследит я и поразит в море силу его, и той огнем поястся.
5 Ashkelon za tă ga haka ta ji tsoro; Gaza za tă yi birgima cikin azaba, haka Ekron ma, gama za tă fid da zuciya. Gaza za tă rasa sarkinta za a kuma gudu a bar Ashkelon.
Увидит Аскалон и убоится, и Газа и поболит зело, и Аккарон, яко постыдеся о уповании своем: и погибнет царь от Газы, и Аскалон не имать населитися.
6 Baƙi za su mallaki Ashdod, kuma zan kawar da girman kan Filistiyawa.
И вселятся иноплеменницы во Азоте, и разрушу досаждение иноплеменников,
7 Zan kawar da jini daga bakinsu, zan kuma cire abincin da aka haramta daga tsakanin haƙoransu. Waɗanda za a bari za su zama na Allahnmu, su kuma zama shugabanni a Yahuda, Ekron kuma za tă zama kamar Yebusiyawa.
и изму кровь их из уст их и мерзости их из средины зубов их, и оставятся и сии Богу нашему и будут яко тысящник во Иуде, и Аккарон якоже Иевусей.
8 Amma zan kāre gidana daga sojoji masu kai da kawowa. Azzalumi ba zai ƙara cin mutanena da yaƙi ba, gama yanzu ina tsaro.
И подставлю храму Моему воздвижение, еже не сквозе ходити, ниже возвращатися, и ктому не имать приити на ня изгоняяй: яко ныне видех очима Моима.
9 Ki yi murna ƙwarai, ya Diyar Urushalima! Ki yi sowa, Diyar Urushalima! Duba, ga sarkinki yana zuwa wurinki, mai adalci yana kuma da ceto, mai tawali’u yana kuma hawan jaki, yana a kan ɗan aholaki, a kan’yar jaka.
Радуйся зело, дщи Сионя, проповедуй, дщи Иерусалимля: се, Царь твой грядет тебе праведен и спасаяй, той кроток и всед на подяремника и жребца юна.
10 Zan ƙwace kekunan yaƙi daga Efraim, da kuma dawakan yaƙi daga Urushalima, za a kuma karya bakan yaƙi. Zai yi shelar salama ga al’ummai. Mulkinsa zai yaɗu daga teku zuwa teku, daga Kogi kuma zuwa ƙarshen duniya.
И потребит колесницы от Ефрема и кони от Иерусалима, и потребит лук бранный, и множество, и мир от языков: и обладает водами от моря до моря и от рек до исходищ земли.
11 Ke kuma, saboda jinin alkawarina da ke, zan’yantar da’yan kurkukunki daga rami marar ruwa.
И ты в крови завета твоего испустил еси узники твоя от рова не имуща воды.
12 Ku koma maɓuya, ya ku’yan kurkuku masu sa zuciya; ko yanzu ma na sanar cewa zan mayar muku ninki biyu.
Сядите в тверделех, связани сонмища, и за един день пришелствия твоего сугубо воздам ти.
13 Zan lanƙwasa Yahuda yadda nake lanƙwasa bakana, in kuma cika ta da Efraim kamar kibiya. Zan tā da’ya’yanki maza, ya Sihiyona, gāba da’ya’yanki, ya Girka, in kuma mai da ke kamar takobin jarumin yaƙi.
Занеже напрягох тя Себе, Иудо, яко лук, исполних Ефрема, и воздвигну чада твоя, Сионе, на чада Еллинска, и осяжу тя яко мечь ратника.
14 Sa’an nan Ubangiji zai bayyana a bisansu; kibiyarsa za tă wulga kamar walƙiya. Ubangiji Mai Iko Duka zai busa ƙaho; zai taho ta cikin guguwa daga kudu,
И Господь на них явится, и изыдет яко молния стрела Его: и Господь Бог Вседержитель в трубу вострубит и пойдет в шуме прещения своего.
15 Ubangiji Maɗaukaki kuma zai tsare su. Za su hallakar su kuma yi nasara da duwatsun majajjawa. Za su sha su yi kururuwa kamar sun sha ruwan inabi; za su cika kamar kwanon da ake amfani don a yayyafa jini a kusurwoyin bagade.
Господь Вседержитель защитит их, и поядят я, и посыплют их камением пращным, и испиют кровь их яко вино, и исполнят окрины яко жертвенник.
16 Ubangiji Allahnsu zai cece su a wannan rana gama su mutanensa ne da kuma garkensa. Za su haska a cikin ƙasarsa kamar lu’ulu’u a rawani.
И спасет я Господь Бог их в день он, яко овцы люди Своя: зане камение свято валяется на земли Его.
17 Za su yi kyan gani da kuma bansha’awa! Hatsi zai sa samari su yi murna, sabon ruwan inabi kuma zai sa’yan mata su yi farin ciki.
Аще что благо его, и аще что добро его, пшеница юношам и вино благоуханно девам.