< Zakariya 9 >

1 Annabci. Maganar Ubangiji tana gāba da ƙasar Hadrak za tă kuma sauko a kan Damaskus, gama idanun dukan mutane da na kabilan Isra’ila suna a kan Ubangiji,
Sentence Parole de Yahweh contre le pays d’Hadrach; et à Damas sera son séjour, — car Yahweh a l’œil sur les hommes, et sur toutes les tribus d’Israël; —
2 da kuma a kan Hamat ita ma, wadda ta yi iyaka da ita, da kuma a kan Taya da Sidon, ko da yake suna da hikima ƙwarai.
et aussi à Hamath, voisine de Damas, à Tyr, ainsi qu’à Sidon, parce que leur sagesse est grande.
3 Taya ta gina wa kanta mafaka mai ƙarfi; ta tara azurfa kamar ƙasa, zinariya kuma kamar tarin shara a tituna.
Tyr s’est construit une citadelle, elle a amassé l’argent comme la poussière, et l’or comme la boue des rues.
4 Amma Ubangiji zai karɓe mallakarta, zai hallaka ikonta da take da shi a kan teku, wuta kuma za tă cinye ta.
Voici que le Seigneur s’en emparera; il frappera sur mer sa puissance, et elle-même sera dévorée par le feu.
5 Ashkelon za tă ga haka ta ji tsoro; Gaza za tă yi birgima cikin azaba, haka Ekron ma, gama za tă fid da zuciya. Gaza za tă rasa sarkinta za a kuma gudu a bar Ashkelon.
Ascalon le verra et craindra; Gaza aussi, et elle se tordra de douleur; Accaron aussi, car son espérance est confondue. Il n’y aura plus de roi à Gaza, et Ascalon ne sera plus habitée.
6 Baƙi za su mallaki Ashdod, kuma zan kawar da girman kan Filistiyawa.
Un vil étranger s’installera à Azoth, et je détruirai l’orgueil des Philistins.
7 Zan kawar da jini daga bakinsu, zan kuma cire abincin da aka haramta daga tsakanin haƙoransu. Waɗanda za a bari za su zama na Allahnmu, su kuma zama shugabanni a Yahuda, Ekron kuma za tă zama kamar Yebusiyawa.
J’ôterai son sang de sa bouche, et ses abominations d’entre ses dents; et lui aussi sera un reste pour notre Dieu; il sera comme un chefen Juda; et Accaron sera comme le Jébuséen.
8 Amma zan kāre gidana daga sojoji masu kai da kawowa. Azzalumi ba zai ƙara cin mutanena da yaƙi ba, gama yanzu ina tsaro.
Je camperai autour de ma maison pour la défendre; contre toute armée, tout allant et venant; et il ne passera plus chez eux d’oppresseur, car maintenant j’ai vu de mes yeux.
9 Ki yi murna ƙwarai, ya Diyar Urushalima! Ki yi sowa, Diyar Urushalima! Duba, ga sarkinki yana zuwa wurinki, mai adalci yana kuma da ceto, mai tawali’u yana kuma hawan jaki, yana a kan ɗan aholaki, a kan’yar jaka.
Tressaille d’une grande joie, fille de Sion! Pousse des cris d’allégresse, fille de Jérusalem! Voici que ton Roi vient à toi; il est juste, lui, et protégé de Dieu; il est humble; monté sur un âne, et sur un poulain, petit d’une ânesse.
10 Zan ƙwace kekunan yaƙi daga Efraim, da kuma dawakan yaƙi daga Urushalima, za a kuma karya bakan yaƙi. Zai yi shelar salama ga al’ummai. Mulkinsa zai yaɗu daga teku zuwa teku, daga Kogi kuma zuwa ƙarshen duniya.
Je retrancherai d’Ephraïm les chars de guerre, et de Jérusalem les chevaux, et l’arc du combat sera détruit. Il parlera de paix aux nations; sa domination s’étendra d’une mer à l’autre, du fleuve jusqu’aux extrémités de la terre.
11 Ke kuma, saboda jinin alkawarina da ke, zan’yantar da’yan kurkukunki daga rami marar ruwa.
Pour toi aussi, à cause du sang de ton alliance, je retirerai tes captifs de la fosse sans eau.
12 Ku koma maɓuya, ya ku’yan kurkuku masu sa zuciya; ko yanzu ma na sanar cewa zan mayar muku ninki biyu.
Revenez au lieu fort, captifs d’espérance! Aujourd’hui encore je le déclare: je te rendrai au double.
13 Zan lanƙwasa Yahuda yadda nake lanƙwasa bakana, in kuma cika ta da Efraim kamar kibiya. Zan tā da’ya’yanki maza, ya Sihiyona, gāba da’ya’yanki, ya Girka, in kuma mai da ke kamar takobin jarumin yaƙi.
Car je bande pour moi Juda, et sur l’arc je place Ephraïm; j’exciterai tes fils, ô Sion, contre tes fils, ô Javan, et je ferai de toi comme une épée de vaillant.
14 Sa’an nan Ubangiji zai bayyana a bisansu; kibiyarsa za tă wulga kamar walƙiya. Ubangiji Mai Iko Duka zai busa ƙaho; zai taho ta cikin guguwa daga kudu,
Yahweh apparaîtra au-dessus d’eux, sa flèche partira comme l’éclair; le Seigneur Yahweh sonnera de la trompette, et s’avancera dans les ouragans du midi.
15 Ubangiji Maɗaukaki kuma zai tsare su. Za su hallakar su kuma yi nasara da duwatsun majajjawa. Za su sha su yi kururuwa kamar sun sha ruwan inabi; za su cika kamar kwanon da ake amfani don a yayyafa jini a kusurwoyin bagade.
Yahweh des armées les protégera; Ils dévoreront, ils fouleront aux pieds les pierres de fronde; Ils boiront, ils se démèneront comme pris de vin, et ils seront remplis comme la coupe des sacrifices, comme les cornes de l’autel.
16 Ubangiji Allahnsu zai cece su a wannan rana gama su mutanensa ne da kuma garkensa. Za su haska a cikin ƙasarsa kamar lu’ulu’u a rawani.
Yahweh leur Dieu sera leur salut en ce jour-là, le salut du troupeau qui est son peuple; ils seront comme des pierres de diadème, qui brilleront dans son pays.
17 Za su yi kyan gani da kuma bansha’awa! Hatsi zai sa samari su yi murna, sabon ruwan inabi kuma zai sa’yan mata su yi farin ciki.
Quelle prospérité, quelle beauté que la leur! Le froment fera croître les jeunes gens, et le vin nouveau les vierges.

< Zakariya 9 >