< Zakariya 9 >

1 Annabci. Maganar Ubangiji tana gāba da ƙasar Hadrak za tă kuma sauko a kan Damaskus, gama idanun dukan mutane da na kabilan Isra’ila suna a kan Ubangiji,
[the] oracle of [the] word of Yahweh [is] on [the] land of Hadrach and Damascus [is] resting place its for [is] to Yahweh [the] eye of humankind and all [the] tribes of Israel.
2 da kuma a kan Hamat ita ma, wadda ta yi iyaka da ita, da kuma a kan Taya da Sidon, ko da yake suna da hikima ƙwarai.
And also Hamath [which] it borders it Tyre and Sidon for it is wise exceedingly.
3 Taya ta gina wa kanta mafaka mai ƙarfi; ta tara azurfa kamar ƙasa, zinariya kuma kamar tarin shara a tituna.
And it built Tyre a fortification for itself and it heaped up silver like dust and gold like [the] mud of [the] streets.
4 Amma Ubangiji zai karɓe mallakarta, zai hallaka ikonta da take da shi a kan teku, wuta kuma za tă cinye ta.
There! [the] Lord he will dispossess it and he will strike in the sea wealth its and it by fire it will be consumed.
5 Ashkelon za tă ga haka ta ji tsoro; Gaza za tă yi birgima cikin azaba, haka Ekron ma, gama za tă fid da zuciya. Gaza za tă rasa sarkinta za a kuma gudu a bar Ashkelon.
It will see Ashkelon so it may be afraid and Gaza so it may be in anguish exceedingly and Ekron for it will be ashamed object of confidence its and he will perish a king from Gaza and Ashkelon not it will remain.
6 Baƙi za su mallaki Ashdod, kuma zan kawar da girman kan Filistiyawa.
And it will dwell a mixed population in Ashdod and I will cut off [the] pride of [the] Philistines.
7 Zan kawar da jini daga bakinsu, zan kuma cire abincin da aka haramta daga tsakanin haƙoransu. Waɗanda za a bari za su zama na Allahnmu, su kuma zama shugabanni a Yahuda, Ekron kuma za tă zama kamar Yebusiyawa.
And I will remove blood its from mouth its and detestable things its from between teeth its and it will be left also it to God our and it will be like a chief in Judah and Ekron [will be] like a Jebusite.
8 Amma zan kāre gidana daga sojoji masu kai da kawowa. Azzalumi ba zai ƙara cin mutanena da yaƙi ba, gama yanzu ina tsaro.
And I will encamp for house my a guard from [one who] passes through and from [one who] returns and not he will pass over them again an oppressor for now I have seen with own eyes my.
9 Ki yi murna ƙwarai, ya Diyar Urushalima! Ki yi sowa, Diyar Urushalima! Duba, ga sarkinki yana zuwa wurinki, mai adalci yana kuma da ceto, mai tawali’u yana kuma hawan jaki, yana a kan ɗan aholaki, a kan’yar jaka.
Rejoice exceedingly O daughter of Zion shout for joy O daughter of Jerusalem there! king your he will come to you [is] righteous and victorious he poor and riding on a donkey and on a male donkey a young one of female donkeys.
10 Zan ƙwace kekunan yaƙi daga Efraim, da kuma dawakan yaƙi daga Urushalima, za a kuma karya bakan yaƙi. Zai yi shelar salama ga al’ummai. Mulkinsa zai yaɗu daga teku zuwa teku, daga Kogi kuma zuwa ƙarshen duniya.
And I will cut off chariotry from Ephraim and horse[s] from Jerusalem and it will be cut off bow of war and he will speak peace to the nations and dominion his [will be] from sea to sea and from [the] river to [the] ends of [the] earth.
11 Ke kuma, saboda jinin alkawarina da ke, zan’yantar da’yan kurkukunki daga rami marar ruwa.
Also you by [the] blood of covenant your I will set free prisoners your from a pit [which] not water [is] in it.
12 Ku koma maɓuya, ya ku’yan kurkuku masu sa zuciya; ko yanzu ma na sanar cewa zan mayar muku ninki biyu.
Return to [the] stronghold O prisoners of hope also this day [I am] declaring double I will restore to you.
13 Zan lanƙwasa Yahuda yadda nake lanƙwasa bakana, in kuma cika ta da Efraim kamar kibiya. Zan tā da’ya’yanki maza, ya Sihiyona, gāba da’ya’yanki, ya Girka, in kuma mai da ke kamar takobin jarumin yaƙi.
For I will bend for myself Judah a bow I will fill Ephraim and I will rouse sons your O Zion on sons your O Greece and I will make you like [the] sword of a warrior.
14 Sa’an nan Ubangiji zai bayyana a bisansu; kibiyarsa za tă wulga kamar walƙiya. Ubangiji Mai Iko Duka zai busa ƙaho; zai taho ta cikin guguwa daga kudu,
And Yahweh over them he will appear and it will go forth like lightning arrow his and [the] Lord Yahweh on the ram's horn he will give a blast and he will go in [the] storm winds of [the] south.
15 Ubangiji Maɗaukaki kuma zai tsare su. Za su hallakar su kuma yi nasara da duwatsun majajjawa. Za su sha su yi kururuwa kamar sun sha ruwan inabi; za su cika kamar kwanon da ake amfani don a yayyafa jini a kusurwoyin bagade.
Yahweh of hosts he will defend them and they will eat and they will subdue stones of a sling and they will drink they will be in an uproar like wine and they will be full like bowl like [the] corners of [the] altar.
16 Ubangiji Allahnsu zai cece su a wannan rana gama su mutanensa ne da kuma garkensa. Za su haska a cikin ƙasarsa kamar lu’ulu’u a rawani.
And he will deliver them Yahweh God their on the day that like [the] flock of people his for stones of a crown [will] display themselves on land his.
17 Za su yi kyan gani da kuma bansha’awa! Hatsi zai sa samari su yi murna, sabon ruwan inabi kuma zai sa’yan mata su yi farin ciki.
For how! [will be] goodness its and how! [will be] beauty its grain young men and new wine it will cause to thrive young women.

< Zakariya 9 >