< Zakariya 9 >
1 Annabci. Maganar Ubangiji tana gāba da ƙasar Hadrak za tă kuma sauko a kan Damaskus, gama idanun dukan mutane da na kabilan Isra’ila suna a kan Ubangiji,
The burden of the word of the Lord in the land of Hadrach, and of Damascus the rest thereof: for the eye of man, and of all the tribes of Israel is the Lord’s.
2 da kuma a kan Hamat ita ma, wadda ta yi iyaka da ita, da kuma a kan Taya da Sidon, ko da yake suna da hikima ƙwarai.
Emath also in the borders thereof, and Tyre, and Sidon: for they have taken to themselves to be exceeding wise.
3 Taya ta gina wa kanta mafaka mai ƙarfi; ta tara azurfa kamar ƙasa, zinariya kuma kamar tarin shara a tituna.
And Tyre hath built herself a strong hold, and heaped together silver as earth, and gold as the mire of the streets.
4 Amma Ubangiji zai karɓe mallakarta, zai hallaka ikonta da take da shi a kan teku, wuta kuma za tă cinye ta.
Behold the Lord shall possess her, and shall strike her strength in the sea, and she shall be devoured with fire.
5 Ashkelon za tă ga haka ta ji tsoro; Gaza za tă yi birgima cikin azaba, haka Ekron ma, gama za tă fid da zuciya. Gaza za tă rasa sarkinta za a kuma gudu a bar Ashkelon.
Ascalon shall see, and shall fear, and Gaza, and shall be very sorrowful: and Accaron, because her hope is confounded: and the king shall perish from Gaza, and Ascalon shall not be inhabited.
6 Baƙi za su mallaki Ashdod, kuma zan kawar da girman kan Filistiyawa.
And the divider shall sit in Azotus, and I will destroy the pride of the Philistines.
7 Zan kawar da jini daga bakinsu, zan kuma cire abincin da aka haramta daga tsakanin haƙoransu. Waɗanda za a bari za su zama na Allahnmu, su kuma zama shugabanni a Yahuda, Ekron kuma za tă zama kamar Yebusiyawa.
And I will take away his blood out of his mouth, and his abominations from between his teeth: and even he shall be left to our God, and he shall be as a governor in Juda, and Accaron as a Jebusite.
8 Amma zan kāre gidana daga sojoji masu kai da kawowa. Azzalumi ba zai ƙara cin mutanena da yaƙi ba, gama yanzu ina tsaro.
And I will encompass my house with them that serve me in war, going and returning, and the oppressor shall no more pass through them: for now I have seen with my eyes.
9 Ki yi murna ƙwarai, ya Diyar Urushalima! Ki yi sowa, Diyar Urushalima! Duba, ga sarkinki yana zuwa wurinki, mai adalci yana kuma da ceto, mai tawali’u yana kuma hawan jaki, yana a kan ɗan aholaki, a kan’yar jaka.
Rejoice greatly, O daughter of Sion, shout for joy, O daughter of Jerusalem: BEHOLD THY KING will come to thee, the just and saviour: he is poor, and riding upon an ass, and upon a colt the foal of an ass.
10 Zan ƙwace kekunan yaƙi daga Efraim, da kuma dawakan yaƙi daga Urushalima, za a kuma karya bakan yaƙi. Zai yi shelar salama ga al’ummai. Mulkinsa zai yaɗu daga teku zuwa teku, daga Kogi kuma zuwa ƙarshen duniya.
And I will destroy the chariot out of Ephraim, and the horse out of Jerusalem, and the bow for war shall be broken: and he shall speak peace to the Gentiles, and his power shall be from sea to sea, and from the rivers even to the end of the earth.
11 Ke kuma, saboda jinin alkawarina da ke, zan’yantar da’yan kurkukunki daga rami marar ruwa.
Thou also by the blood of thy testament hast sent forth thy prisoners out of the pit, wherein is no water.
12 Ku koma maɓuya, ya ku’yan kurkuku masu sa zuciya; ko yanzu ma na sanar cewa zan mayar muku ninki biyu.
Return to the strong hold, ye prisoners of hope, I will render thee double at, I declare today.
13 Zan lanƙwasa Yahuda yadda nake lanƙwasa bakana, in kuma cika ta da Efraim kamar kibiya. Zan tā da’ya’yanki maza, ya Sihiyona, gāba da’ya’yanki, ya Girka, in kuma mai da ke kamar takobin jarumin yaƙi.
Because I have bent Juda for me as a bow, I have filled Ephraim: and I will raise up thy sons, O Sion, above thy sons, O Greece, and I will make thee as the sword of the mighty.
14 Sa’an nan Ubangiji zai bayyana a bisansu; kibiyarsa za tă wulga kamar walƙiya. Ubangiji Mai Iko Duka zai busa ƙaho; zai taho ta cikin guguwa daga kudu,
And the Lord God shall be seen over them, and his dart shall go forth as lightning: and the Lord God will sound the trumpet, and go in the whirlwind of the south.
15 Ubangiji Maɗaukaki kuma zai tsare su. Za su hallakar su kuma yi nasara da duwatsun majajjawa. Za su sha su yi kururuwa kamar sun sha ruwan inabi; za su cika kamar kwanon da ake amfani don a yayyafa jini a kusurwoyin bagade.
The Lord of hosts will protect them: and they shall devour, and subdue with the stones of the sling: and drinking they shall be inebriated as it were with wine, and they shall be filled as bowls, and as the horns of the altar.
16 Ubangiji Allahnsu zai cece su a wannan rana gama su mutanensa ne da kuma garkensa. Za su haska a cikin ƙasarsa kamar lu’ulu’u a rawani.
And the Lord their God will save them in that day, as the dock of his people: for holy stones shall be lifted up over his land.
17 Za su yi kyan gani da kuma bansha’awa! Hatsi zai sa samari su yi murna, sabon ruwan inabi kuma zai sa’yan mata su yi farin ciki.
For what is the good thing of him, and what is his beautiful thing, but the corn of the elect, and wine springing forth virgins?