< Zakariya 8 >
1 Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa gare ni.
Opet doðe rijeè Gospoda nad vojskama govoreæi:
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ina kishin Sihiyona ƙwarai; ina kuma cike da kishi dominta.”
Ovako veli Gospod nad vojskama: revnujem za Sion velikom revnošæu, i velikim gnjevom revnujem za nj.
3 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Zan koma Sihiyona in zauna a Urushalima. Sa’an nan za a kira Urushalima Birnin Gaskiya, a kuma kira dutsen Ubangiji Maɗaukaki Dutse Mai Tsarki.”
Ovako veli Gospod: vratih se u Sion i naselih se usred Jerusalima, i Jerusalim æe se zvati grad istiniti, i gora Gospoda nad vojskama sveta gora.
4 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Tsofaffi maza da mata za su sāke zauna a titunan Urushalima, kowanne da sanda a hannu saboda tsufa.
Ovako veli Gospod nad vojskama: opet æe sjedjeti starci i starice po ulicama Jerusalimskim, svatko sa štakom u ruci od velike starosti.
5 Titunan birnin za su cika da samari da’yan mata suna wasa.”
I ulice æe gradske biti pune djetiæa i djevojaka, koje æe se igrati po ulicama.
6 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mai yiwuwa ya zama da mamaki ga raguwar wannan mutanen da suke nan a lokacin, amma zai zama abin mamaki gare ni ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
Ovako veli Gospod nad vojskama: ako je èudno u oèima ostatku toga naroda u ovo vrijeme, eda li æe biti èudno i u mojim oèima? govori Gospod nad vojskama.
7 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Zan ceci mutanena daga ƙasashen gabas da yamma.
Ovako veli Gospod nad vojskama: evo, ja æu izbaviti svoj narod iz zemlje istoène i iz zemlje zapadne.
8 Zan komo da su su zauna a Urushalima; za su zama mutanena, ni kuwa zan zama amintaccen Allahnsu mai adalci.”
I dovešæu ih, i oni æe nastavati usred Jerusalima, i biæe mi narod i ja æu im biti Bog, istinom i pravdom.
9 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku da yanzu kuke jin maganan nan da annabawa suka faɗi, waɗanda suke a nan lokacin da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji Maɗaukaki, bari hannuwanku su zama da ƙarfi don a gama gina haikalin.
Ovako veli Gospod nad vojskama: neka vam se ukrijepe ruke koji slušate u ovo vrijeme ove rijeèi iz usta proroèkih od dana kad se osnova dom Gospoda nad vojskama da se sazida crkva.
10 Kafin wannan lokaci babu albashi domin mutum ko dabba. Ba wanda yake iya sakewa yă yi hidimominsa saboda maƙiya, domin na sa kowa yă zama maƙiyi maƙwabcinsa.
Jer prije tijeh dana ne bješe plate ni za èovjeka ni za živinèe, niti bješe mira od neprijatelja ni onome koji odlažaše ni onome koji dolažaše, i pustih sve ljude jednoga na drugoga.
11 Amma yanzu ba zan yi da waɗanda raguwar mutane yadda na yi da na dā ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
A sada neæu biti kao prije ostatku toga naroda, govori Gospod nad vojskama.
12 “Iri zai yi girma da kyau, kuringa za tă ba da’ya’yanta, ƙasa za tă ba da hatsi, sama kuma za tă ba da raɓa. Zan ba da duk waɗannan abubuwa su zama gādo ga raguwar mutanen nan.
Nego æe usjev biti miran, vinova æe loza nositi plod svoj, i zemlja æe raðati rod svoj, i nebo æe davati rosu svoju; i sve æu to dati u našljedstvo ostatku toga naroda.
13 Kamar yadda kuka zama abin la’ana a ƙasashe, ya Yahuda da Isra’ila, haka zan cece ku, za ku kuma zama albarka. Kada ku ji tsoro, sai dai ku bar hannuwanku su zama da ƙarfi.”
I kao što bijaste uklin meðu narodima, dome Judin i dome Izrailjev, tako æu vas izbaviti te æete biti blagoslov; ne bojte se, neka vam se okrijepe ruke.
14 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Kamar dai yadda na yi niyyar kawo muku bala’i, in kuma ƙi jin tausayi sa’ad da kakanninku suka ba ni haushi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki,
Jer ovako veli Gospod nad vojskama: kao što vam namislih zlo uèiniti, kad me razgnjeviše oci vaši, veli Gospod nad vojskama, i ne raskajah se,
15 kada ku ji tsoro “saboda a yanzu na yi niyya in sāke yi wa Urushalima da Yahuda abu mai kyau.
Tako opet u ove dane namislih da dobro èinim Jerusalimu i domu Judinu; ne bojte se.
16 Abubuwan da za ku yi ke nan. Ku gaya wa juna gaskiya, ku kuma dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunanku na shari’arku;
Ovo je što treba da èinite: govorite istinu jedan drugom, sudite pravo i mirno na vratima svojim;
17 kada ku ƙulla wa maƙwabtanku mugunta, kuma kada ku so yin rantsuwa ta ƙarya. Ina ƙyamar waɗannan duka,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
I ne mislite jedan drugome zlo u srcu svom, i ne ljubite krive zakletve, jer na sve to mrzim, govori Gospod.
18 Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa wurina.
Potom doðe mi rijeè Gospoda nad vojskama govoreæi:
19 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Azumin wata na huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai da na watan goma za su zama lokutan farin ciki da murna da kuma bukukkuwa na murna ga Yahuda. Saboda haka sai ku ƙaunaci gaskiya da salama.”
Ovako veli Gospod nad vojskama: post èetvrtoga mjeseca, i post petoga i post sedmoga i post desetoga obratiæe se domu Judinu u radost i veselje i u praznike vesele; ali ljubite istinu i mir.
20 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mutane da yawa da kuma mazaunan birane da yawa har yanzu za su zo,
Ovako veli Gospod nad vojskama: još æe dolaziti narodi i stanovnici mnogih gradova;
21 mazaunan wani birni za su je wurin mazaunan wani birni su ce, ‘Bari mu je nan da nan mu roƙi Ubangiji mu kuma nemi Ubangiji Maɗaukaki. Ni kaina zan je.’
Dolaziæe stanovnici jednoga u drugi govoreæi: hajdemo da se molimo Gospodu i da tražimo Gospoda nad vojskama; idem i ja.
22 Mutane da yawa kuma da al’ummai masu ƙarfi za su zo Urushalima su nemi Ubangiji Maɗaukaki su kuma roƙe shi.”
Tako æe doæi mnogi narodi i silni narodi da traže Gospoda nad vojskama u Jerusalimu i da se mole Gospodu.
23 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “A kwanakin nan, mutane goma daga kabilu da al’ummai za su riƙe rigar mutumin Yahuda guda su ce, ‘Bari mu tafi tare da kai, domin mun ji cewa Allah yana tare da ku.’”
Ovako veli Gospod nad vojskama: u to æe vrijeme deset ljudi od svijeh jezika narodnijeh uhvatiti jednoga Judejca za skut govoreæi: idemo s vama, jer èujemo da je Bog s vama.