< Zakariya 8 >

1 Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa gare ni.
A palavra de Yahweh dos Exércitos veio até mim.
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ina kishin Sihiyona ƙwarai; ina kuma cike da kishi dominta.”
Yahweh dos Exércitos diz: “Tenho inveja de Sião com grande ciúme, e tenho inveja dela com grande cólera”.
3 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Zan koma Sihiyona in zauna a Urushalima. Sa’an nan za a kira Urushalima Birnin Gaskiya, a kuma kira dutsen Ubangiji Maɗaukaki Dutse Mai Tsarki.”
Yahweh diz: “Eu voltei a Sião, e habitarei no meio de Jerusalém. Jerusalém será chamada 'A Cidade da Verdade'; e a montanha de Yahweh dos Exércitos, 'A Montanha Santa'”.
4 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Tsofaffi maza da mata za su sāke zauna a titunan Urushalima, kowanne da sanda a hannu saboda tsufa.
Yahweh dos exércitos diz: “Velhos homens e velhas mulheres voltarão a morar nas ruas de Jerusalém, cada homem com seu bastão na mão por causa de sua velhice.
5 Titunan birnin za su cika da samari da’yan mata suna wasa.”
As ruas da cidade estarão cheias de meninos e meninas brincando em suas ruas”.
6 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mai yiwuwa ya zama da mamaki ga raguwar wannan mutanen da suke nan a lokacin, amma zai zama abin mamaki gare ni ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
Yahweh dos Exércitos diz: “Se é maravilhoso aos olhos do resto deste povo naqueles dias, deveria ser também maravilhoso aos meus olhos?” diz Yahweh dos Exércitos.
7 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Zan ceci mutanena daga ƙasashen gabas da yamma.
Yahweh dos Exércitos diz: “Eis que salvarei meu povo do país oriental e do país ocidental”.
8 Zan komo da su su zauna a Urushalima; za su zama mutanena, ni kuwa zan zama amintaccen Allahnsu mai adalci.”
Eu os trarei, e eles morarão dentro de Jerusalém. Eles serão meu povo, e eu serei seu Deus, em verdade e em justiça”.
9 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku da yanzu kuke jin maganan nan da annabawa suka faɗi, waɗanda suke a nan lokacin da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji Maɗaukaki, bari hannuwanku su zama da ƙarfi don a gama gina haikalin.
Yahweh dos Exércitos diz: “Que vossas mãos sejam fortes, vós que ouvis nestes dias estas palavras da boca dos profetas que estavam no dia em que foi lançada a fundação da casa de Yahweh dos Exércitos, até mesmo o templo, para que ele pudesse ser construído”.
10 Kafin wannan lokaci babu albashi domin mutum ko dabba. Ba wanda yake iya sakewa yă yi hidimominsa saboda maƙiya, domin na sa kowa yă zama maƙiyi maƙwabcinsa.
Pois antes daqueles dias não havia salário para o homem, nem salário para um animal, nem paz para aquele que saía ou entrava, por causa do adversário. Pois eu coloco todos os homens contra o seu próximo.
11 Amma yanzu ba zan yi da waɗanda raguwar mutane yadda na yi da na dā ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Mas agora eu não serei para o resto deste povo como nos dias anteriores”, diz Yahweh dos Exércitos.
12 “Iri zai yi girma da kyau, kuringa za tă ba da’ya’yanta, ƙasa za tă ba da hatsi, sama kuma za tă ba da raɓa. Zan ba da duk waɗannan abubuwa su zama gādo ga raguwar mutanen nan.
“Pois a semente da paz e da videira dará seus frutos, e a terra dará seu aumento, e os céus darão seu orvalho”. Farei com que o resto deste povo herde todas estas coisas”.
13 Kamar yadda kuka zama abin la’ana a ƙasashe, ya Yahuda da Isra’ila, haka zan cece ku, za ku kuma zama albarka. Kada ku ji tsoro, sai dai ku bar hannuwanku su zama da ƙarfi.”
Acontecerá que, como vós fostes uma maldição entre as nações, casa de Judá e casa de Israel, assim eu vos salvarei, e sereis uma bênção. Não tenhais medo. Deixai que vossas mãos sejam fortes”.
14 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Kamar dai yadda na yi niyyar kawo muku bala’i, in kuma ƙi jin tausayi sa’ad da kakanninku suka ba ni haushi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki,
Para Javé dos Exércitos diz: “Como eu pensava em fazer o mal a vocês quando seus pais me provocaram à ira”, diz Javé dos Exércitos, “e eu não me arrependi,
15 kada ku ji tsoro “saboda a yanzu na yi niyya in sāke yi wa Urushalima da Yahuda abu mai kyau.
então novamente pensei nestes dias em fazer o bem a Jerusalém e à casa de Judá”. Não tenha medo”.
16 Abubuwan da za ku yi ke nan. Ku gaya wa juna gaskiya, ku kuma dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunanku na shari’arku;
Estas são as coisas que você deve fazer: falar a verdade a cada homem com seu próximo. Executem o julgamento da verdade e da paz em seus portões,
17 kada ku ƙulla wa maƙwabtanku mugunta, kuma kada ku so yin rantsuwa ta ƙarya. Ina ƙyamar waɗannan duka,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
e não deixem que nenhum de vocês invente o mal em seus corações contra seu próximo, e não amem nenhum falso juramento; pois tudo isso são coisas que eu odeio”, diz Javé.
18 Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa wurina.
A palavra de Yahweh dos Exércitos veio até mim.
19 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Azumin wata na huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai da na watan goma za su zama lokutan farin ciki da murna da kuma bukukkuwa na murna ga Yahuda. Saboda haka sai ku ƙaunaci gaskiya da salama.”
Yahweh dos Exércitos diz: “O jejum do quarto, quinto, sétimo e décimo mês será para a casa de Judá alegria, alegria e festas alegres”. Portanto, amai a verdade e a paz”.
20 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mutane da yawa da kuma mazaunan birane da yawa har yanzu za su zo,
Yahweh dos Exércitos diz: “Muitos povos e os habitantes de muitas cidades ainda virão”.
21 mazaunan wani birni za su je wurin mazaunan wani birni su ce, ‘Bari mu je nan da nan mu roƙi Ubangiji mu kuma nemi Ubangiji Maɗaukaki. Ni kaina zan je.’
Os habitantes de uma irão para outra, dizendo: 'Vamos rapidamente pedir o favor de Javé e buscar o Javé dos Exércitos'. Eu irei também”.
22 Mutane da yawa kuma da al’ummai masu ƙarfi za su zo Urushalima su nemi Ubangiji Maɗaukaki su kuma roƙe shi.”
Yes, muitos povos e nações fortes virão para buscar o Iavé dos Exércitos em Jerusalém e para implorar o favor de Iavé”.
23 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “A kwanakin nan, mutane goma daga kabilu da al’ummai za su riƙe rigar mutumin Yahuda guda su ce, ‘Bari mu tafi tare da kai, domin mun ji cewa Allah yana tare da ku.’”
Yahweh dos Exércitos diz: “Naqueles dias, dez homens de todas as línguas das nações se apoderarão da saia daquele que é judeu, dizendo: 'Iremos com vocês, pois ouvimos dizer que Deus está com vocês'”.

< Zakariya 8 >