< Zakariya 8 >
1 Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa gare ni.
Depois veiu a mim a palavra do Senhor dos Exercitos, dizendo:
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ina kishin Sihiyona ƙwarai; ina kuma cike da kishi dominta.”
Assim diz o Senhor dos Exercitos: Zelei por Sião com grande zelo, e com grande furor zelei por ella.
3 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Zan koma Sihiyona in zauna a Urushalima. Sa’an nan za a kira Urushalima Birnin Gaskiya, a kuma kira dutsen Ubangiji Maɗaukaki Dutse Mai Tsarki.”
Assim diz o Senhor: Voltarei para Sião, e habitarei no meio de Jerusalem; e Jerusalem chamar-se-ha a cidade de verdade, e o monte do Senhor dos Exercitos monte de sanctidade.
4 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Tsofaffi maza da mata za su sāke zauna a titunan Urushalima, kowanne da sanda a hannu saboda tsufa.
Assim diz o Senhor dos Exercitos: Ainda nas praças de Jerusalem habitarão velhos e velhas; e cada um terá na sua mão o seu bordão, por causa da sua muita edade.
5 Titunan birnin za su cika da samari da’yan mata suna wasa.”
E as ruas da cidade serão cheias de meninos e meninas, que brincarão nas ruas d'ella.
6 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mai yiwuwa ya zama da mamaki ga raguwar wannan mutanen da suke nan a lokacin, amma zai zama abin mamaki gare ni ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
Assim diz o Senhor dos Exercitos: Se isto será maravilhoso aos olhos do resto d'este povo n'aquelles dias, sel-o-ha por isso tambem maravilhoso aos meus olhos? disse o Senhor dos Exercitos.
7 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Zan ceci mutanena daga ƙasashen gabas da yamma.
Assim diz o Senhor dos Exercitos: Eis que salvarei o meu povo da terra do oriente e da terra do pôr do sol;
8 Zan komo da su su zauna a Urushalima; za su zama mutanena, ni kuwa zan zama amintaccen Allahnsu mai adalci.”
E tral-os-hei, e habitarão no meio de Jerusalem; e me serão por povo, e eu lhes serei a elles por Deus em verdade e em justiça.
9 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku da yanzu kuke jin maganan nan da annabawa suka faɗi, waɗanda suke a nan lokacin da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji Maɗaukaki, bari hannuwanku su zama da ƙarfi don a gama gina haikalin.
Assim diz o Senhor dos Exercitos: Esforcem-se as vossas mãos, ó vós que n'estes dias ouvistes estas palavras da bocca dos prophetas que estiveram no dia em que foi posto o fundamento da casa do Senhor dos Exercitos, para que o templo fosse edificado.
10 Kafin wannan lokaci babu albashi domin mutum ko dabba. Ba wanda yake iya sakewa yă yi hidimominsa saboda maƙiya, domin na sa kowa yă zama maƙiyi maƙwabcinsa.
Porque antes d'estes dias não tem havido soldada de homens, nem soldada de bestas; nem havia paz para o que entrava nem para o que sahia, por causa do inimigo, porque eu incitei a todos os homens, cada um contra o seu companheiro.
11 Amma yanzu ba zan yi da waɗanda raguwar mutane yadda na yi da na dā ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Mas agora não me haverei eu para com o resto d'este povo como nos primeiros dias, diz o Senhor dos Exercitos.
12 “Iri zai yi girma da kyau, kuringa za tă ba da’ya’yanta, ƙasa za tă ba da hatsi, sama kuma za tă ba da raɓa. Zan ba da duk waɗannan abubuwa su zama gādo ga raguwar mutanen nan.
Porque a semente será prospera, a vide dará o seu fructo, e a terra dará a sua novidade, e os céus darão o seu orvalho; e farei que o resto d'este povo herde tudo isto
13 Kamar yadda kuka zama abin la’ana a ƙasashe, ya Yahuda da Isra’ila, haka zan cece ku, za ku kuma zama albarka. Kada ku ji tsoro, sai dai ku bar hannuwanku su zama da ƙarfi.”
E ha de ser, ó casa de Judah, e ó casa de Israel, que, assim como fostes uma maldição entre as nações, assim vos salvarei, e sereis uma benção: não temaes, esforcem-se as vossas mãos.
14 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Kamar dai yadda na yi niyyar kawo muku bala’i, in kuma ƙi jin tausayi sa’ad da kakanninku suka ba ni haushi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki,
Porque assim diz o Senhor dos Exercitos: Assim como pensei fazer-vos mal, quando vossos paes me provocaram á ira, diz o Senhor dos Exercitos, e não me arrependi,
15 kada ku ji tsoro “saboda a yanzu na yi niyya in sāke yi wa Urushalima da Yahuda abu mai kyau.
Assim tornei a pensar de fazer bem a Jerusalem e á casa de Judah, n'estes dias: não temaes.
16 Abubuwan da za ku yi ke nan. Ku gaya wa juna gaskiya, ku kuma dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunanku na shari’arku;
Estas são as coisas que fareis: Fallae verdade cada um com o seu companheiro; julgae verdade e juizo de paz nas vossas portas.
17 kada ku ƙulla wa maƙwabtanku mugunta, kuma kada ku so yin rantsuwa ta ƙarya. Ina ƙyamar waɗannan duka,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
E nenhum de vós pense mal no seu coração contra o seu companheiro, nem ameis o juramento falso; porque todas estas coisas são as que eu aborreço, diz o Senhor.
18 Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa wurina.
E a palavra do Senhor dos Exercitos veiu a mim, dizendo:
19 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Azumin wata na huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai da na watan goma za su zama lokutan farin ciki da murna da kuma bukukkuwa na murna ga Yahuda. Saboda haka sai ku ƙaunaci gaskiya da salama.”
Assim diz o Senhor dos Exercitos: O jejum do quarto, e o jejum do quinto, e o jejum do setimo, e o jejum do decimo mez se tornará para a casa de Judah em gozo, e em alegria, e em festividades solemnes: amae pois a verdade e a paz.
20 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mutane da yawa da kuma mazaunan birane da yawa har yanzu za su zo,
Assim diz o Senhor dos Exercitos: Ainda succederá que virão os povos e os habitantes de muitas cidades.
21 mazaunan wani birni za su je wurin mazaunan wani birni su ce, ‘Bari mu je nan da nan mu roƙi Ubangiji mu kuma nemi Ubangiji Maɗaukaki. Ni kaina zan je.’
E os habitantes de uma irão á outra, dizendo: Vamos andando para supplicar a face do Senhor, e para buscar ao Senhor dos Exercitos; eu tambem irei.
22 Mutane da yawa kuma da al’ummai masu ƙarfi za su zo Urushalima su nemi Ubangiji Maɗaukaki su kuma roƙe shi.”
Assim virão muitos povos e poderosas nações, a buscar em Jerusalem ao Senhor dos Exercitos, e a supplicar a face do Senhor.
23 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “A kwanakin nan, mutane goma daga kabilu da al’ummai za su riƙe rigar mutumin Yahuda guda su ce, ‘Bari mu tafi tare da kai, domin mun ji cewa Allah yana tare da ku.’”
Assim diz o Senhor dos Exercitos: N'aquelle dia succederá que pegarão dez homens de entre todas as linguas das nações, pegarão, digo, da aba de um homem judaico, dizendo: Iremos comvosco, porque temos ouvido que Deus está comvosco.