< Zakariya 8 >
1 Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa gare ni.
Et la parole du Seigneur des armées me fut adressée, disant:
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ina kishin Sihiyona ƙwarai; ina kuma cike da kishi dominta.”
Voici ce que dit le Seigneur des armées: J’ai été zélé pour Sion d’un grand zèle, et j’ai été animé contre elle d’une grande indignation.
3 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Zan koma Sihiyona in zauna a Urushalima. Sa’an nan za a kira Urushalima Birnin Gaskiya, a kuma kira dutsen Ubangiji Maɗaukaki Dutse Mai Tsarki.”
Voici ce que dit le Seigneur des armées: Je suis revenu à Sion, et j’habiterai au milieu de Jérusalem; et Jérusalem sera appelée la cité de la vérité, et la montagne du Dieu des armées, la montagne sainte.
4 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Tsofaffi maza da mata za su sāke zauna a titunan Urushalima, kowanne da sanda a hannu saboda tsufa.
Voici ce que dit le Seigneur des armées: Des vieillards et des vieilles femmes habiteront encore sur les places de Jérusalem, et des hommes, chacun un bâton en sa main, à cause de la multitude de leurs jours.
5 Titunan birnin za su cika da samari da’yan mata suna wasa.”
Et les places de la cité seront remplies de petits garçons et de petites filles qui joueront sur ses places.
6 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mai yiwuwa ya zama da mamaki ga raguwar wannan mutanen da suke nan a lokacin, amma zai zama abin mamaki gare ni ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
Voici ce que dit le Seigneur des armées: Si ma prédiction paraît difficile aux yeux des restes de ce peuple en ces jours-là, est-ce qu’à mes yeux elle sera difficile, dit le Seigneur des armées?
7 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Zan ceci mutanena daga ƙasashen gabas da yamma.
Voici ce que dit le Seigneur des armées: Voici que moi, je sauverai mon peuple de la terre de l’orient et de la terre du coucher du soleil.
8 Zan komo da su su zauna a Urushalima; za su zama mutanena, ni kuwa zan zama amintaccen Allahnsu mai adalci.”
Et je les ramènerai, et ils habiteront au milieu de Jérusalem; et ils seront mon peuple, et moi je serai leur Dieu, dans la vérité et dans la justice.
9 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku da yanzu kuke jin maganan nan da annabawa suka faɗi, waɗanda suke a nan lokacin da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji Maɗaukaki, bari hannuwanku su zama da ƙarfi don a gama gina haikalin.
Voici ce que dit le Seigneur des armées: Que vos mains se fortifient, vous qui entendez en ces jours ces paroles par la bouche des prophètes, au jour auquel a été fondée la maison du Seigneur des armées, afin que le temple fût bâti.
10 Kafin wannan lokaci babu albashi domin mutum ko dabba. Ba wanda yake iya sakewa yă yi hidimominsa saboda maƙiya, domin na sa kowa yă zama maƙiyi maƙwabcinsa.
Car avant ces jours-là, il n’y avait pas de récompense pour les hommes, ni de récompense pour les bêtes; et pour celui qui entrait et pour celui qui sortait, il n’y avait pas de paix à cause de la tribulation; et j’abandonnai tous les hommes chacun contre son prochain.
11 Amma yanzu ba zan yi da waɗanda raguwar mutane yadda na yi da na dā ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Mais maintenant ce ne sera pas comme aux jours antérieurs que moi je traiterai les restes de ce peuple, dit le Seigneur des armées.
12 “Iri zai yi girma da kyau, kuringa za tă ba da’ya’yanta, ƙasa za tă ba da hatsi, sama kuma za tă ba da raɓa. Zan ba da duk waɗannan abubuwa su zama gādo ga raguwar mutanen nan.
Mais il y aura une semence de paix; la vigne donnera son fruit, et la terre donnera ses productions, et les deux donneront leur rosée; et je ferai posséder tous ces biens aux restes de ce peuple.
13 Kamar yadda kuka zama abin la’ana a ƙasashe, ya Yahuda da Isra’ila, haka zan cece ku, za ku kuma zama albarka. Kada ku ji tsoro, sai dai ku bar hannuwanku su zama da ƙarfi.”
Et il arrivera que comme vous étiez un objet de malédiction parmi les nations, maison de Juda et maison d’Israël, ainsi je vous sauverai, et vous serez un objet de bénédiction; ne craignez point; que vos mains se fortifient.
14 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Kamar dai yadda na yi niyyar kawo muku bala’i, in kuma ƙi jin tausayi sa’ad da kakanninku suka ba ni haushi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki,
Parce que voici ce que dit le Seigneur des armées: Comme j’ai songé à vous punir, lorsque vos pères m’ont provoqué au courroux, dit le Seigneur,
15 kada ku ji tsoro “saboda a yanzu na yi niyya in sāke yi wa Urushalima da Yahuda abu mai kyau.
Et que je n’ai pas eu de pitié; ainsi, revenu à eux, j’ai songé en ces jours à faire du bien à la maison de Juda et à Jérusalem; ne craignez point.
16 Abubuwan da za ku yi ke nan. Ku gaya wa juna gaskiya, ku kuma dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunanku na shari’arku;
Voici donc ce que vous ferez: Parlez vérité, chacun avec son prochain; jugez selon la vérité, et rendez des jugements de paix à vos portes.
17 kada ku ƙulla wa maƙwabtanku mugunta, kuma kada ku so yin rantsuwa ta ƙarya. Ina ƙyamar waɗannan duka,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Qu’aucun de vous ne médite en son cœur le mal contre son ami; et n’aimez pas le serment mensonger; car ce sont toutes choses que je hais, dit le Seigneur.
18 Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa wurina.
Et la parole du Seigneur des armées me fut adressée, disant:
19 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Azumin wata na huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai da na watan goma za su zama lokutan farin ciki da murna da kuma bukukkuwa na murna ga Yahuda. Saboda haka sai ku ƙaunaci gaskiya da salama.”
Voici ce que dit le Seigneur des armées: Le jeûne du quatrième mois, et le jeûne du cinquième, et le jeûne du septième, et le jeûne du dixième seront changés pour la maison de Juda en joie et en allégresse, et en solennités brillantes; aimez seulement la vérité et la paix.
20 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mutane da yawa da kuma mazaunan birane da yawa har yanzu za su zo,
Voici ce que dit le Seigneur des armées: Que des peuples viennent encore, et qu’ils habitent dans beaucoup de cités;
21 mazaunan wani birni za su je wurin mazaunan wani birni su ce, ‘Bari mu je nan da nan mu roƙi Ubangiji mu kuma nemi Ubangiji Maɗaukaki. Ni kaina zan je.’
Et que les habitants aillent l’un vers l’autre, disant: Allons, et implorons la face du Seigneur, et cherchons le Seigneur des armées; j’irai, moi aussi.
22 Mutane da yawa kuma da al’ummai masu ƙarfi za su zo Urushalima su nemi Ubangiji Maɗaukaki su kuma roƙe shi.”
Et beaucoup de peuples viendront ainsi que des nations puissantes pour chercher le Seigneur des armées dans Jérusalem, et pour implorer la face du Seigneur.
23 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “A kwanakin nan, mutane goma daga kabilu da al’ummai za su riƙe rigar mutumin Yahuda guda su ce, ‘Bari mu tafi tare da kai, domin mun ji cewa Allah yana tare da ku.’”
Voici ce que dit le Seigneur des armées: Ceci arrivera en ces jours-là, dans lesquels dix hommes de toutes les langues des nations, saisiront la frange de la robe d’un homme juif, disant: Nous irons avec vous, car nous avons appris que Dieu est avec vous.