< Zakariya 8 >

1 Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa gare ni.
La parole de l'Eternel des armées me fut encore [adressée], en disant:
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ina kishin Sihiyona ƙwarai; ina kuma cike da kishi dominta.”
Ainsi a dit l'Eternel des armées: J'ai été jaloux pour Sion d'une grande jalousie, et j'ai été jaloux pour elle avec une grande indignation.
3 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Zan koma Sihiyona in zauna a Urushalima. Sa’an nan za a kira Urushalima Birnin Gaskiya, a kuma kira dutsen Ubangiji Maɗaukaki Dutse Mai Tsarki.”
Ainsi a dit l'Eternel: Je me suis retourné vers Sion, et j'habiterai au milieu de Jérusalem; et Jérusalem sera appelée, Ville de vérité; et la montagne de l'Eternel des armées [sera appelée], montagne de sainteté.
4 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Tsofaffi maza da mata za su sāke zauna a titunan Urushalima, kowanne da sanda a hannu saboda tsufa.
Ainsi a dit l'Eternel des armées: Il demeurera encore des vieillards et des vieilles femmes dans les places de Jérusalem, et chacun aura son bâton à la main à cause de son grand âge.
5 Titunan birnin za su cika da samari da’yan mata suna wasa.”
Et les place de la ville seront remplies de fils et de filles, qui se joueront dans ses places.
6 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mai yiwuwa ya zama da mamaki ga raguwar wannan mutanen da suke nan a lokacin, amma zai zama abin mamaki gare ni ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
Ainsi a dit l'Eternel des armées: S'il semble difficile devant les yeux du reste de ce peuple, [que cela arrive] en ces jours-là, sera-t-il pourtant difficile devant mes yeux, Dit l'Eternel des armées?
7 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Zan ceci mutanena daga ƙasashen gabas da yamma.
Ainsi a dit l'Eternel des armées: Voici, je m'en vais délivrer mon peuple du pays de l'Orient, et du pays du soleil couchant;
8 Zan komo da su su zauna a Urushalima; za su zama mutanena, ni kuwa zan zama amintaccen Allahnsu mai adalci.”
Et je les ferai venir et ils habiteront dans Jérusalem, et ils seront mon peuple, et je serai leur Dieu en vérité et en justice.
9 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku da yanzu kuke jin maganan nan da annabawa suka faɗi, waɗanda suke a nan lokacin da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji Maɗaukaki, bari hannuwanku su zama da ƙarfi don a gama gina haikalin.
Ainsi a dit l'Eternel des armées: Vous qui entendez en ces jours-ci ces paroles de la bouche des Prophètes qui ont été au jour que la maison de l'Eternel a été fondée, et le Temple rebâti, que vos mains soient fortifiées.
10 Kafin wannan lokaci babu albashi domin mutum ko dabba. Ba wanda yake iya sakewa yă yi hidimominsa saboda maƙiya, domin na sa kowa yă zama maƙiyi maƙwabcinsa.
Car avant ces jours-ci il n'y avait point de salaire pour l'homme, ni de salaire pour la bête; et il n'y avait point de paix pour les allants, ni pour les venants, à cause de la détresse, et j'envoyais tous les hommes l'un contre l'autre.
11 Amma yanzu ba zan yi da waɗanda raguwar mutane yadda na yi da na dā ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Mais maintenant je ne [ferai] point à ceux qui sont restés de ce peuple, comme [j'ai fait] les jours précédents; dit l'Eternel des armées.
12 “Iri zai yi girma da kyau, kuringa za tă ba da’ya’yanta, ƙasa za tă ba da hatsi, sama kuma za tă ba da raɓa. Zan ba da duk waɗannan abubuwa su zama gādo ga raguwar mutanen nan.
Mais ce [qu'ils sèmeront] sera une semence de prospérité, la semence de paix [sera là]; la vigne rendra son fruit, et la terre donnera son rapport; les cieux donneront leur rosée, et je ferai hériter toutes ces choses à ceux qui seront restés de ce peuple.
13 Kamar yadda kuka zama abin la’ana a ƙasashe, ya Yahuda da Isra’ila, haka zan cece ku, za ku kuma zama albarka. Kada ku ji tsoro, sai dai ku bar hannuwanku su zama da ƙarfi.”
Et il arrivera, ô maison de Juda et maison d'Israël! Que comme vous avez été en malédiction parmi les nations, ainsi je vous en délivrerai, et vous serez en bénédiction; ne craignez point, [mais] que vos mains soient fortifiées.
14 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Kamar dai yadda na yi niyyar kawo muku bala’i, in kuma ƙi jin tausayi sa’ad da kakanninku suka ba ni haushi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki,
Car ainsi a dit l'Eternel des armées: Comme j'ai pensé de vous affliger, quand vos pères ont provoqué mon indignation, dit l'Eternel des armées, et je ne m'en suis point repenti;
15 kada ku ji tsoro “saboda a yanzu na yi niyya in sāke yi wa Urushalima da Yahuda abu mai kyau.
Ainsi au contraire je me suis retourné, et j'ai pensé en ces jours-ci de faire du bien à Jérusalem, et à la maison de Juda; ne craignez point.
16 Abubuwan da za ku yi ke nan. Ku gaya wa juna gaskiya, ku kuma dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunanku na shari’arku;
[Et] ce sont ici les choses que vous devez faire: Parlez en vérité, chacun avec son prochain; prononcez la vérité et un jugement de paix dans vos portes.
17 kada ku ƙulla wa maƙwabtanku mugunta, kuma kada ku so yin rantsuwa ta ƙarya. Ina ƙyamar waɗannan duka,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Et que personne ne machine du mal dans son cœur contre son prochain; et n'aimez point le faux serment: car ce sont là des choses que je hais, dit l'Eternel.
18 Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa wurina.
Puis la parole de l'Eternel des armées me fut [adressée], en disant:
19 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Azumin wata na huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai da na watan goma za su zama lokutan farin ciki da murna da kuma bukukkuwa na murna ga Yahuda. Saboda haka sai ku ƙaunaci gaskiya da salama.”
Ainsi a dit l'Eternel des armées: Le jeûne du quatrième mois, et le jeûne du cinquième, et le jeûne du septième, et le jeûne du dixième, seront changés pour la maison de Juda en joie et en allégresse, et en des fêtes solennelles de réjouissance; aimez donc la vérité et la paix.
20 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mutane da yawa da kuma mazaunan birane da yawa har yanzu za su zo,
Ainsi a dit l'Eternel des armées: Encore il arrivera que les peuples et les habitants de plusieurs villes viendront;
21 mazaunan wani birni za su je wurin mazaunan wani birni su ce, ‘Bari mu je nan da nan mu roƙi Ubangiji mu kuma nemi Ubangiji Maɗaukaki. Ni kaina zan je.’
Et que les habitants de l'une iront à l'autre, en disant: Allons, allons supplier l'Eternel, et rechercher l'Eternel des armées; Je m'y en irai moi aussi.
22 Mutane da yawa kuma da al’ummai masu ƙarfi za su zo Urushalima su nemi Ubangiji Maɗaukaki su kuma roƙe shi.”
Ainsi plusieurs peuples, et de puissantes nations viendront rechercher l'Eternel des armées à Jérusalem, et y supplier l'Eternel.
23 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “A kwanakin nan, mutane goma daga kabilu da al’ummai za su riƙe rigar mutumin Yahuda guda su ce, ‘Bari mu tafi tare da kai, domin mun ji cewa Allah yana tare da ku.’”
Ainsi a dit l'Eternel des armées: Il arrivera en ces jours-là que dix hommes de toutes les langues des nations empoigneront et tiendront ferme le pan de la robe d'un Juif, en disant: Nous irons avec vous; car nous avons entendu que Dieu est avec vous.

< Zakariya 8 >