< Zakariya 8 >
1 Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa gare ni.
Hærskarers HERRES Ord kom saaledes:
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ina kishin Sihiyona ƙwarai; ina kuma cike da kishi dominta.”
Saa siger Hærskarers HERRE: Jeg er fuld af Nidkærhed for Zion, ja i stor Vrede er jeg nidkær for det.
3 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Zan koma Sihiyona in zauna a Urushalima. Sa’an nan za a kira Urushalima Birnin Gaskiya, a kuma kira dutsen Ubangiji Maɗaukaki Dutse Mai Tsarki.”
Saa siger HERREN: Jeg vender tilbage til Zion og fæster Bo i Jerusalem; Jerusalem skal kaldes den trofaste By, og Hærskarers HERRES Bjerg det hellige Bjerg.
4 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Tsofaffi maza da mata za su sāke zauna a titunan Urushalima, kowanne da sanda a hannu saboda tsufa.
Saa siger Hærskarers HERRE: Atter skal gamle Mænd og Kvinder sidde paa Jerusalems Torve, alle med Stav i Haand for deres Ældes Skyld,
5 Titunan birnin za su cika da samari da’yan mata suna wasa.”
og Byens Torve skal vrimle af legende Drenge og Piger.
6 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mai yiwuwa ya zama da mamaki ga raguwar wannan mutanen da suke nan a lokacin, amma zai zama abin mamaki gare ni ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
Saa siger Hærskarers HERRE: Fordi det i disse Dage synes det tiloversblevne af dette Folk umuligt, skulde det saa ogsaa synes mig umuligt, lyder det fra Hærskarers HERRE.
7 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Zan ceci mutanena daga ƙasashen gabas da yamma.
Saa siger Hærskarers HERRE: Se, jeg frelser mit Folk fra Østerleden og Vesterleden
8 Zan komo da su su zauna a Urushalima; za su zama mutanena, ni kuwa zan zama amintaccen Allahnsu mai adalci.”
og fører dem hjem, og de skal bo i Jerusalem og være mit Folk, og jeg vil være deres Gud i Trofasthed og Retfærd.
9 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku da yanzu kuke jin maganan nan da annabawa suka faɗi, waɗanda suke a nan lokacin da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji Maɗaukaki, bari hannuwanku su zama da ƙarfi don a gama gina haikalin.
Saa siger Hærskarers HERRE: Fat Mod, I, som i denne Tid hører disse Ord af Profeternes Mund, fra den Dag Grunden lagdes til Hærskarers HERRES Hus, Helligdommen, som skulde bygges.
10 Kafin wannan lokaci babu albashi domin mutum ko dabba. Ba wanda yake iya sakewa yă yi hidimominsa saboda maƙiya, domin na sa kowa yă zama maƙiyi maƙwabcinsa.
Thi før disse Dage gav hverken Menneskers eller Kvægs Arbejde Udbytte; de, som drog ud og ind, havde ikke Fred for Fjenden, og jeg slap alle Mennesker løs paa hverandre.
11 Amma yanzu ba zan yi da waɗanda raguwar mutane yadda na yi da na dā ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Men nu er jeg ikke mod det tiloversblevne af dette Folk som i fordums Dage, lyder det fra Hærskarers HERRE;
12 “Iri zai yi girma da kyau, kuringa za tă ba da’ya’yanta, ƙasa za tă ba da hatsi, sama kuma za tă ba da raɓa. Zan ba da duk waɗannan abubuwa su zama gādo ga raguwar mutanen nan.
jeg udsaar Fred, Vinstokken skal give sin Frugt, Jorden sin Afgrøde og Himmelen sin Dug, og jeg giver det tiloversblevne af dette Folk det alt sammen i Eje.
13 Kamar yadda kuka zama abin la’ana a ƙasashe, ya Yahuda da Isra’ila, haka zan cece ku, za ku kuma zama albarka. Kada ku ji tsoro, sai dai ku bar hannuwanku su zama da ƙarfi.”
Og som I, baade Judas og Israels Hus, har været et Forbandelsens Tegn blandt Folkene, saaledes skal I, naar jeg har frelst eder, blive et Velsignelsens. Frygt ikke, fat Mod!
14 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Kamar dai yadda na yi niyyar kawo muku bala’i, in kuma ƙi jin tausayi sa’ad da kakanninku suka ba ni haushi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki,
Thi saa siger Hærskarers HERRE: Som jeg, da eders Fædre vakte min Vrede, satte mig for at handle ilde med eder og ikke angrede det, siger Hærskarers HERRE,
15 kada ku ji tsoro “saboda a yanzu na yi niyya in sāke yi wa Urushalima da Yahuda abu mai kyau.
saaledes har jeg nu i disse Dage omvendt sat mig for at gøre vel mod Jerusalem og Judas Hus. Frygt ikke!
16 Abubuwan da za ku yi ke nan. Ku gaya wa juna gaskiya, ku kuma dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunanku na shari’arku;
Men hvad I skal gøre, er dette: Tal Sandhed hver med sin Næste, fæld i eders Porte Domme, der hviler paa Sandhed og fører til Fred,
17 kada ku ƙulla wa maƙwabtanku mugunta, kuma kada ku so yin rantsuwa ta ƙarya. Ina ƙyamar waɗannan duka,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
tænk ikke i eders Hjerter ondt mod hverandre og elsk ikke falske Eder! Thi alt sligt hader jeg, lyder det fra HERREN.
18 Maganar Ubangiji Maɗaukaki ta sāke zuwa wurina.
Og Hærskarers HERRES Ord kom til mig saaledes:
19 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Azumin wata na huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai da na watan goma za su zama lokutan farin ciki da murna da kuma bukukkuwa na murna ga Yahuda. Saboda haka sai ku ƙaunaci gaskiya da salama.”
Saa siger Hærskarers HERRE: Fasten i den fjerde, femte, syvende og tiende Maaned skal blive Judas Hus til Fryd og Glæde og gode Højtidsdage. Elsk Sandhed og Fred!
20 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Mutane da yawa da kuma mazaunan birane da yawa har yanzu za su zo,
Saa siger Hærskarers HERRE: Endnu skal det ske, at Folkeslag og mange Byers Indbyggere skal komme,
21 mazaunan wani birni za su je wurin mazaunan wani birni su ce, ‘Bari mu je nan da nan mu roƙi Ubangiji mu kuma nemi Ubangiji Maɗaukaki. Ni kaina zan je.’
og den ene Bys Indbyggere skal gaa til den andens og sige: »Lad os vandre hen og bede HERREN om Naade og søge Hærskarers HERRE; ogsaa jeg vil med.«
22 Mutane da yawa kuma da al’ummai masu ƙarfi za su zo Urushalima su nemi Ubangiji Maɗaukaki su kuma roƙe shi.”
Og mange Folkeslag og talrige Folk skal komme og søge Hærskarers HERRE i Jerusalem for at bede HERREN om Naade.
23 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “A kwanakin nan, mutane goma daga kabilu da al’ummai za su riƙe rigar mutumin Yahuda guda su ce, ‘Bari mu tafi tare da kai, domin mun ji cewa Allah yana tare da ku.’”
Saa siger Hærskarers HERRE: I hine Dage skal ti Mænd af alle Folks Tungemaal gribe fat i en Jødes Kappeflig og sige: »Vi vil gaa med eder; thi vi har hørt, at Gud er med eder.«