< Zakariya 7 >

1 A shekara ta huɗu ta Sarki Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa Zakariya a rana ta huɗu ta watan tara, wato, watan Kisleb.
Kral Darius'un krallığının dördüncü yılının dokuzuncu ayı olan Kislev ayının dördüncü günü RAB Zekeriya'ya seslendi.
2 Mutanen Betel sun aika Sharezer da Regem-Melek, tare da mutanensu su nemi tagomashin Ubangiji
Beytel halkı, Her Şeye Egemen RAB'bin Tapınağı'ndaki kâhinlerle peygamberlere, “Yıllardır yaptığımız gibi beşinci ay oruç tutup ağlayalım mı?” diye sormuş ve RAB'be yalvarmaları için Sareser'i, Regem-Melek'i ve adamlarını göndermişti.
3 ta wurin tambayar firistocin da kuma annabawan gidan Ubangiji Maɗaukaki, “Ko ya kamata in yi makoki da azumi a wata na biyar, yadda na yi a shekaru masu yawa?”
4 Sai maganar Ubangiji Maɗaukaki ta zo mini ta ce,
Her Şeye Egemen RAB bana dedi ki,
5 “Ka tambayi dukan mutanen ƙasar da firistoci cewa, ‘Sa’ad da kuka yi makoki da azumi a wata na biyar da na bakwai dukan shekaru saba’in nan, a ainihi saboda ni kuka yi azumi?
“Bütün ülke halkına ve kâhinlere sor: ‘Yetmiş yıldır beşinci ve yedinci aylarda oruç tutup dövündüğünüzde gerçekten benim için mi oruç tuttunuz?
6 Kuma sa’ad da kuke ci kuke sha, ba kanku kuke yi wa shagali ba?
Yiyip içerken kendiniz için yiyip içmiyor muydunuz?
7 Ashe, ba kalmomin da Ubangiji ya faɗi ke nan ta bakin annabawan farko ba sa’ad da Urushalima da garuruwan da suke kewaye da ita suke hutawa, suke cikin wadata, akwai kuma mutane a Negeb da yammancin gindin tuddai?’”
Yeruşalim'le çevresindeki kentler gönenç içinde yaşarken, Negev ve Şefela insanlarla doluyken, RAB'bin önceki peygamberler aracılığıyla açıkladığı sözler bunlar değil mi?’”
8 Sai maganar Ubangiji ta sāke zuwa wa Zakariya cewa,
RAB Zekeriya'ya yine seslendi:
9 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku yi shari’ar gaskiya; ku nuna jinƙai da tausayi ga juna.
“Her Şeye Egemen RAB diyor ki, ‘Gerçek adaletle yargılayın; birbirinize sevgi ve sevecenlik gösterin.
10 Kada ku danne gwauruwa ko maraya, baƙo ko talaka. A cikin zuciyarku kada ku yi mugun tunani game da juna.’
Dul kadına, öksüze, yabancıya, yoksula baskı yapmayın. Yüreğinizde birbirinize karşı kötülük tasarlamayın.’
11 “Amma suka ƙi su saurara; da taurinkai suka juya bayansu suka kuma toshe kunnuwansu.
“Ama atalarımız dinlemek istemediler; inatla sırtlarını çevirdiler, duymamak için kulaklarını tıkadılar.
12 Suka taurare zukatansu kamar dutse, suka ƙi jin abin da doka ko kuma maganar Ubangiji Maɗaukaki take faɗi wadda ya aika ta wurin Ruhunsa ta wurin annabawan farko. Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki ya ji fushi ƙwarai.
Kutsal Yasa'yı ve Her Şeye Egemen RAB'bin kendi Ruhu'yla gönderdiği, önceki peygamberler aracılığıyla ilettiği sözleri dinlememek için yüreklerini taş gibi sertleştirdiler. Bu yüzden Her Şeye Egemen RAB onlara çok öfkelendi.
13 “‘Sa’ad da na yi kira, ba su saurara ba; saboda haka sa’ad da suka kira, ba zan saurara ba,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
“‘Madem ben çağırınca dinlemediler’ diyor Her Şeye Egemen RAB, ‘Onlar çağırınca, ben de onları dinlemeyeceğim.
14 ‘Na warwatsar da su da guguwa a cikin dukan ƙasashe, inda suka zama baƙi. Aka bar ƙasar ta zama kango bayansu, da har ba mai shiga ko fita. Haka suka sa ƙasan nan mai daɗi ta zama kango.’”
Onları tanımadıkları ulusların arasına fırtına gibi dağıttım. Geride bıraktıkları ülke öyle ıssız kaldı ki, oraya kimse gidip gelemez oldu. Güzelim ülkeyi viraneye çevirdiler.’”

< Zakariya 7 >