< Zakariya 7 >
1 A shekara ta huɗu ta Sarki Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa Zakariya a rana ta huɗu ta watan tara, wato, watan Kisleb.
And it came to pass in the fourth year of king Darius that the word of the Lord came unto Zechariah on the fourth day of the ninth month, in Kislev;
2 Mutanen Betel sun aika Sharezer da Regem-Melek, tare da mutanensu su nemi tagomashin Ubangiji
When they had sent unto Beth-el Sherezer and Regem-melech, and his men, to make entreaty before the Lord.
3 ta wurin tambayar firistocin da kuma annabawan gidan Ubangiji Maɗaukaki, “Ko ya kamata in yi makoki da azumi a wata na biyar, yadda na yi a shekaru masu yawa?”
[And] to say unto the priests who were in the house of the Lord of hosts, and to the prophets, saying, Shall I weep in the fifth month with abstinence, as I have done already these many years?
4 Sai maganar Ubangiji Maɗaukaki ta zo mini ta ce,
Then came the word of the Lord of hosts unto me, saying,
5 “Ka tambayi dukan mutanen ƙasar da firistoci cewa, ‘Sa’ad da kuka yi makoki da azumi a wata na biyar da na bakwai dukan shekaru saba’in nan, a ainihi saboda ni kuka yi azumi?
Say unto all the people of the land, and to the priests, as followeth, When ye fasted and mourned in the fifth and in the seventh [month], already these seventy years, did ye in anywise fast for me, yea, for me?
6 Kuma sa’ad da kuke ci kuke sha, ba kanku kuke yi wa shagali ba?
And if ye do eat, and if ye do drink, are ye not yourselves those that eat, and yourselves those that drink?
7 Ashe, ba kalmomin da Ubangiji ya faɗi ke nan ta bakin annabawan farko ba sa’ad da Urushalima da garuruwan da suke kewaye da ita suke hutawa, suke cikin wadata, akwai kuma mutane a Negeb da yammancin gindin tuddai?’”
Are not these the words which the Lord hath proclaimed by means of the former prophets, when Jerusalem was inhabited and in prosperity, with her cities round about her, when [men] inhabited the south, and the lowlands?
8 Sai maganar Ubangiji ta sāke zuwa wa Zakariya cewa,
And the word of the Lord came unto Zechariah, saying,
9 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku yi shari’ar gaskiya; ku nuna jinƙai da tausayi ga juna.
Thus hath said the Lord of hosts, saying, Execute true justice, and show kindness and mercy every man to his brother;
10 Kada ku danne gwauruwa ko maraya, baƙo ko talaka. A cikin zuciyarku kada ku yi mugun tunani game da juna.’
And defraud not the widow, or the fatherless, the stranger, or the poor; and imagine not evil in your heart one against the other.
11 “Amma suka ƙi su saurara; da taurinkai suka juya bayansu suka kuma toshe kunnuwansu.
But they refused to listen, and turned away rebelliously the shoulder, and stopped their ears, so as not to hear;
12 Suka taurare zukatansu kamar dutse, suka ƙi jin abin da doka ko kuma maganar Ubangiji Maɗaukaki take faɗi wadda ya aika ta wurin Ruhunsa ta wurin annabawan farko. Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki ya ji fushi ƙwarai.
And their heart they rendered as an adamant, so as not to hear the law, and the words which the Lord of hosts had sent through his spirit, by means of the former prophets: wherefore came a great anger from the Lord of hosts.
13 “‘Sa’ad da na yi kira, ba su saurara ba; saboda haka sa’ad da suka kira, ba zan saurara ba,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And it is come to pass, that as he proclaimed, and they would not hear: so had they to call, and I would not hear, saith the Lord of hosts;
14 ‘Na warwatsar da su da guguwa a cikin dukan ƙasashe, inda suka zama baƙi. Aka bar ƙasar ta zama kango bayansu, da har ba mai shiga ko fita. Haka suka sa ƙasan nan mai daɗi ta zama kango.’”
And I resolved to scatter them with a storm-wind among all the nations that they had not known; and the land was left desolate after them, without any one to pass through it forward or backward; and the pleasant land have they changed into a desert.