< Zakariya 7 >

1 A shekara ta huɗu ta Sarki Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa Zakariya a rana ta huɗu ta watan tara, wato, watan Kisleb.
And it came to pass in the fourth year of king Darius, that the word of the LORD came unto Zechariah in the fourth day of the ninth month, even in Chislev;
2 Mutanen Betel sun aika Sharezer da Regem-Melek, tare da mutanensu su nemi tagomashin Ubangiji
When Bethel-sarezer, and Regem-melech and his men, had sent to entreat the favour of the LORD,
3 ta wurin tambayar firistocin da kuma annabawan gidan Ubangiji Maɗaukaki, “Ko ya kamata in yi makoki da azumi a wata na biyar, yadda na yi a shekaru masu yawa?”
and to speak unto the priests of the house of the LORD of hosts, and to the prophets, saying: 'Should I weep in the fifth month, separating myself, as I have done these so many years?'
4 Sai maganar Ubangiji Maɗaukaki ta zo mini ta ce,
Then came the word of the LORD of hosts unto me, saying:
5 “Ka tambayi dukan mutanen ƙasar da firistoci cewa, ‘Sa’ad da kuka yi makoki da azumi a wata na biyar da na bakwai dukan shekaru saba’in nan, a ainihi saboda ni kuka yi azumi?
'Speak unto all the people of the land, and to the priests, saying: When ye fasted and mourned in the fifth and in the seventh month, even these seventy years, did ye at all fast unto Me, even to Me?
6 Kuma sa’ad da kuke ci kuke sha, ba kanku kuke yi wa shagali ba?
And when ye eat, and when ye drink, are ye not they that eat, and they that drink?
7 Ashe, ba kalmomin da Ubangiji ya faɗi ke nan ta bakin annabawan farko ba sa’ad da Urushalima da garuruwan da suke kewaye da ita suke hutawa, suke cikin wadata, akwai kuma mutane a Negeb da yammancin gindin tuddai?’”
Should ye not hearken to the words which the LORD hath proclaimed by the former prophets, when Jerusalem was inhabited and in prosperity, and the cities thereof round about her, and the South and the Lowland were inhabited?'
8 Sai maganar Ubangiji ta sāke zuwa wa Zakariya cewa,
And the word of the LORD came unto Zechariah, saying:
9 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku yi shari’ar gaskiya; ku nuna jinƙai da tausayi ga juna.
'Thus hath the LORD of hosts spoken, saying: Execute true judgment, and show mercy and compassion every man to his brother;
10 Kada ku danne gwauruwa ko maraya, baƙo ko talaka. A cikin zuciyarku kada ku yi mugun tunani game da juna.’
and oppress not the widow, nor the fatherless, the stranger, nor the poor; and let none of you devise evil against his brother in your heart.
11 “Amma suka ƙi su saurara; da taurinkai suka juya bayansu suka kuma toshe kunnuwansu.
But they refused to attend, and turned a stubborn shoulder, and stopped their ears, that they might not hear.
12 Suka taurare zukatansu kamar dutse, suka ƙi jin abin da doka ko kuma maganar Ubangiji Maɗaukaki take faɗi wadda ya aika ta wurin Ruhunsa ta wurin annabawan farko. Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki ya ji fushi ƙwarai.
Yea, they made their hearts as an adamant stone, lest they should hear the law, and the words which the LORD of hosts had sent by His spirit by the hand of the former prophets; therefore came there great wrath from the LORD of hosts.
13 “‘Sa’ad da na yi kira, ba su saurara ba; saboda haka sa’ad da suka kira, ba zan saurara ba,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And it came to pass that, as He called, and they would not hear; so they shall call, and I will not hear, said the LORD of hosts;
14 ‘Na warwatsar da su da guguwa a cikin dukan ƙasashe, inda suka zama baƙi. Aka bar ƙasar ta zama kango bayansu, da har ba mai shiga ko fita. Haka suka sa ƙasan nan mai daɗi ta zama kango.’”
but I will scatter them with a whirlwind among all the nations whom they have not known. Thus the land was desolate after them, so that no man passed through nor returned; for they laid the pleasant land desolate.'

< Zakariya 7 >