< Zakariya 6 >

1 Na sāke ɗaga kai sama, sai ga kekunan yaƙi guda huɗu a gabana suna fitowa tsakanin duwatsu guda biyu, duwatsun tagulla!
E outra vez levantei os meus olhos, e olhei, e eis que vi quatro carros que sairam d'entre dois montes, e estes montes eram montes de metal.
2 Karusa ta farko tana da jajjayen dawakai, ta biyu kuma baƙaƙen dawakai,
No primeiro carro eram cavallos vermelhos, e no segundo carro cavallos pretos,
3 ta ukun farare dawakai, ta huɗu kuma dawakai masu ɗigo-ɗigo a dukan jikinsu, dukansu kuwa ƙarfafa.
E no terceiro carro cavallos brancos, e no quarto carro cavallos saraivados, que eram fortes.
4 Sai na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
E respondi, e disse ao anjo que fallava comigo: Que é isto, Senhor meu?
5 Mala’ikan ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ruhohi huɗu na sama, waɗanda suka fito daga wurin Ubangiji na dukan duniya.
E o anjo respondeu, e me disse: Estes são os quatro ventos do céu, saindo d'onde estavam perante o Senhor de toda a terra.
6 Wannan mai baƙaƙen dawakai zai nufi wajen ƙasar arewa, mai fararen dawakai zai nufi wajen yamma, sai kuma mai dawakai masu ɗigo-ɗigo a jiki zai nufi wajen kudu.”
O carro em que estão os cavallos pretos, sae para a terra do norte, e os brancos saem atraz d'elles, e os saraivados saem para a terra do sul.
7 Da ƙarfafa dawakan suka fito, sai suka yi marmari su ratsa dukan duniya. Sai ya ce, “Ku ratsa dukan duniya!” Saboda haka suka ratsa dukan duniya.
E os cavallos fortes sahiam, e procuravam ir por diante, para andarem pela terra. E elle disse: Ide, andae pela terra. E andavam pela terra.
8 Sai ya kira ni ya ce, “Duba, waɗanda suka nufi wajen ƙasar arewa sun ba wa Ruhuna hutu a ƙasar arewa.”
E me chamou, e me fallou, dizendo: Eis que aquelles que sairam para a terra do norte fizeram repousar o meu Espirito na terra do norte.
9 Maganar Ubangiji ta zo mini, ta ce,
E a palavra do Senhor veiu a mim, dizendo:
10 “Ka karɓi azurfa da zinariya daga masu zaman bauta Heldai, Tobiya, Yedahiya, waɗanda suka iso daga Babilon. A ranar kuma ka je gidan Yosiya ɗan Zefaniya.
Toma dos que foram levados captivos: de Heldai, de Tobias, e de Jedaia (e vem n'aquelle dia, e entra na casa de Josias, filho de Sofonias), os quaes vieram de Babylonia.
11 Ka ɗauki azurfar da zinariyar ka yi rawani, ka ɗora shi a kan babban firist, Yoshuwa ɗan Yehozadak.
Toma, digo, prata e oiro, e faze corôas, e põe-as na cabeça de Josué, filho de Josadac, summo sacerdote.
12 Ka ce masa ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ga mutumin da sunansa ne Reshe, zai kuma ratse daga inda yake yă gina haikalin Ubangiji.
E falla-lhe, dizendo: Assim falla o Senhor dos Exercitos, dizendo: Eis aqui o homem cujo nome é o Renovo que brotará do seu logar, e edificará o templo do Senhor.
13 Shi ne zai gina haikalin Ubangiji, za a kuma martaba shi da daraja, zai kuma zauna yă yi mulki a kan kursiyinsa. Zai zama firist a kan kursiyinsa. Kuma a tsakanin biyun za a sami zaman lafiya.’
Elle mesmo edificará o templo do Senhor, e levará elle a gloria, e assentar-se-ha, e dominará no seu throno, e será sacerdote no seu throno, e conselho de paz haverá entre elles ambos.
14 Za a ba Heldai, Tobiya, Yedahiya da kuma Hen ɗan Zefaniya kamar abin tunawa a cikin haikalin Ubangiji.
E estas corôas serão de Helem, e de Tobias, e de Jedaia, e de Chen, filho de Sofonias, por memorial no templo do Senhor.
15 Waɗanda suke nesa za su zo su taimaka gina haikalin Ubangiji, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku. Wannan zai faru in kuka yi biyayya sosai ga Ubangiji Allahnku.”
E aquelles que estão longe virão, e edificarão no templo do Senhor, e vós sabereis que o Senhor dos Exercitos me tem enviado a vós; e isto acontecerá assim, se ouvirdes mui attentos a voz do Senhor vosso Deus.

< Zakariya 6 >