< Zakariya 6 >

1 Na sāke ɗaga kai sama, sai ga kekunan yaƙi guda huɗu a gabana suna fitowa tsakanin duwatsu guda biyu, duwatsun tagulla!
در یک رؤیای دیگر چهار ارابه دیدم که از میان دو کوه مسی بیرون آمدند.
2 Karusa ta farko tana da jajjayen dawakai, ta biyu kuma baƙaƙen dawakai,
ارابهٔ اول به‌وسیلۀ اسبهای سرخ، ارابهٔ دوم به‌وسیلۀ اسبهای سیاه،
3 ta ukun farare dawakai, ta huɗu kuma dawakai masu ɗigo-ɗigo a dukan jikinsu, dukansu kuwa ƙarfafa.
ارابهٔ سوم به‌وسیله اسبهای سفید و ارابهٔ چهارم به‌وسیلۀ اسبهای ابلق کشیده می‌شدند.
4 Sai na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
از فرشته پرسیدم: «ای سرورم، اینها چه هستند؟»
5 Mala’ikan ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ruhohi huɗu na sama, waɗanda suka fito daga wurin Ubangiji na dukan duniya.
جواب داد: «اینها چهار روح آسمانی هستند که در حضور خداوند تمامی زمین می‌ایستند و اینک برای انجام فرمان او به حرکت درآمده‌اند.
6 Wannan mai baƙaƙen dawakai zai nufi wajen ƙasar arewa, mai fararen dawakai zai nufi wajen yamma, sai kuma mai dawakai masu ɗigo-ɗigo a jiki zai nufi wajen kudu.”
اسبهای سیاه به طرف شمال، اسبهای سفید به طرف غرب و اسبهای ابلق به طرف جنوب خواهند رفت.»
7 Da ƙarfafa dawakan suka fito, sai suka yi marmari su ratsa dukan duniya. Sai ya ce, “Ku ratsa dukan duniya!” Saboda haka suka ratsa dukan duniya.
اسبهای قوی بیتابی می‌کردند که حرکت کنند و در سراسر زمین بگردند. خداوند فرمود: «بروید و گشت خود را آغاز کنید.» پس آنها راه افتادند و تمام زمین را گشتند.
8 Sai ya kira ni ya ce, “Duba, waɗanda suka nufi wajen ƙasar arewa sun ba wa Ruhuna hutu a ƙasar arewa.”
آنگاه خداوند مرا احضار کرد و فرمود: «آنهایی که به سرزمین شمال رفتند، حکم مرا اجرا کرده خشم مرا در آنجا فرو نشاندند.»
9 Maganar Ubangiji ta zo mini, ta ce,
در پیامی دیگر خداوند به من فرمود:
10 “Ka karɓi azurfa da zinariya daga masu zaman bauta Heldai, Tobiya, Yedahiya, waɗanda suka iso daga Babilon. A ranar kuma ka je gidan Yosiya ɗan Zefaniya.
«حلدای، طوبیا و یدعیا از طرف یهودیان تبعید شده در بابِل، هدایایی از طلا و نقره آورده‌اند. هدایا را از آنها بگیر و به خانهٔ یوشیا (پسر صفنیا) برو و با آنها تاجی بساز. سپس تاج را بر سر یهوشع (پسر یهوصادق) کاهن اعظم بگذار.
11 Ka ɗauki azurfar da zinariyar ka yi rawani, ka ɗora shi a kan babban firist, Yoshuwa ɗan Yehozadak.
12 Ka ce masa ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ga mutumin da sunansa ne Reshe, zai kuma ratse daga inda yake yă gina haikalin Ubangiji.
به او بگو که خداوند لشکرهای آسمان چنین می‌فرماید:”تو نمونه‌ای هستی از آن مردی که «شاخه» نامیده می‌شود. او از جایی که هست جوانه خواهد زد و خانهٔ خداوند را بازسازی خواهد کرد.
13 Shi ne zai gina haikalin Ubangiji, za a kuma martaba shi da daraja, zai kuma zauna yă yi mulki a kan kursiyinsa. Zai zama firist a kan kursiyinsa. Kuma a tsakanin biyun za a sami zaman lafiya.’
اوست آنکه خانهٔ خداوند را بنا می‌کند و از شکوه پادشاهی برخوردار می‌شود. او در مقام کاهن و پادشاه حکمرانی خواهد کرد، و بین این دو مقام هماهنگی کامل خواهد بود.“
14 Za a ba Heldai, Tobiya, Yedahiya da kuma Hen ɗan Zefaniya kamar abin tunawa a cikin haikalin Ubangiji.
سپس، این تاج را به عنوان هدیه‌ای از طرف حلدای، طوبیا، یدعیا و یوشیا در خانهٔ خداوند بگذار تا یادگاری باشد.»
15 Waɗanda suke nesa za su zo su taimaka gina haikalin Ubangiji, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku. Wannan zai faru in kuka yi biyayya sosai ga Ubangiji Allahnku.”
مردمی که در جاهای دور دست زندگی می‌کنند، خواهند آمد و در بازسازی خانهٔ خداوند کمک خواهند کرد؛ آنگاه خواهید دانست که خداوند لشکرهای آسمان مرا نزد شما فرستاده است. این هنگامی اتفاق خواهد افتاد که شما از خداوند، خدای خویش کاملاً اطاعت کنید.

< Zakariya 6 >