< Zakariya 6 >

1 Na sāke ɗaga kai sama, sai ga kekunan yaƙi guda huɗu a gabana suna fitowa tsakanin duwatsu guda biyu, duwatsun tagulla!
Et je me retournai, et je levai les yeux, et je regardai, et voilà quatre chars sortant entre deux montagnes, et ces montagnes étaient d'airain.
2 Karusa ta farko tana da jajjayen dawakai, ta biyu kuma baƙaƙen dawakai,
Au premier char il y avait des chevaux roux, et au second char, des chevaux noirs,
3 ta ukun farare dawakai, ta huɗu kuma dawakai masu ɗigo-ɗigo a dukan jikinsu, dukansu kuwa ƙarfafa.
et au troisième char, des chevaux blancs, et au quatrième char, des chevaux noirs.
4 Sai na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
Et je parlai, et je dis à l'ange qui parlait avec moi: Qu'est cela, Seigneur?
5 Mala’ikan ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ruhohi huɗu na sama, waɗanda suka fito daga wurin Ubangiji na dukan duniya.
Et l'ange qui parlait avec moi me répondit, et me dit: Ce sont les quatre vents du ciel; ils sortent pour se tenir devant le Seigneur de toute la terre.
6 Wannan mai baƙaƙen dawakai zai nufi wajen ƙasar arewa, mai fararen dawakai zai nufi wajen yamma, sai kuma mai dawakai masu ɗigo-ɗigo a jiki zai nufi wajen kudu.”
Or les chevaux noirs s'en allaient sur toute la terre du septentrion; et les chevaux blancs venaient ensuite; et les gris-pommelé s'en allaient sur la terre du midi;
7 Da ƙarfafa dawakan suka fito, sai suka yi marmari su ratsa dukan duniya. Sai ya ce, “Ku ratsa dukan duniya!” Saboda haka suka ratsa dukan duniya.
et les autres sortirent, et ils regardèrent pour s'en aller et parcourir toute la terre; et l'ange leur dit: Marchez et parcourez toute la terre. Et ils parcoururent toute la terre.
8 Sai ya kira ni ya ce, “Duba, waɗanda suka nufi wajen ƙasar arewa sun ba wa Ruhuna hutu a ƙasar arewa.”
Et il cria, et il me parla, disant: Voilà que ceux qui s'en vont sur la terre du septentrion ont satisfait à Ma colère, en la terre du septentrion.
9 Maganar Ubangiji ta zo mini, ta ce,
Et la parole du Seigneur vint à moi, disant:
10 “Ka karɓi azurfa da zinariya daga masu zaman bauta Heldai, Tobiya, Yedahiya, waɗanda suka iso daga Babilon. A ranar kuma ka je gidan Yosiya ɗan Zefaniya.
Prends les dons des captifs, soit de leurs princes, soit des hommes serviables de la captivité, soit de ceux qui l'honorent; et ce jour-là entre en la maison de Josias, fils de Sophonie, qui est arrivé de Babylone.
11 Ka ɗauki azurfar da zinariyar ka yi rawani, ka ɗora shi a kan babban firist, Yoshuwa ɗan Yehozadak.
Et tu prendras l'argent et l'or, et tu en feras des couronnes, et tu les poseras sur la tête de Jésus, fils de Josédec, le grand prêtre.
12 Ka ce masa ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ga mutumin da sunansa ne Reshe, zai kuma ratse daga inda yake yă gina haikalin Ubangiji.
Et tu lui diras: Voici ce que dit le Seigneur tout-puissant: Voilà un homme: Orient est Son Nom, et Il Se lèvera venant de ce qui est sous Lui.
13 Shi ne zai gina haikalin Ubangiji, za a kuma martaba shi da daraja, zai kuma zauna yă yi mulki a kan kursiyinsa. Zai zama firist a kan kursiyinsa. Kuma a tsakanin biyun za a sami zaman lafiya.’
Et Il bâtira le temple du Seigneur, et Il recevra la force, et Il siégera, et Il régnera sur Son trône; et le prêtre sera à Sa droite, et un conseil de paix sera entre eux deux.
14 Za a ba Heldai, Tobiya, Yedahiya da kuma Hen ɗan Zefaniya kamar abin tunawa a cikin haikalin Ubangiji.
Et la couronne sera pour ceux qui ont souffert patiemment, et pour ceux de la captivité qui auront été serviables, et pour ceux qui l'ont honorée, afin de rendre des actions de grâces au fils de Sophonie; et les chanter dans le temple du Seigneur.
15 Waɗanda suke nesa za su zo su taimaka gina haikalin Ubangiji, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku. Wannan zai faru in kuka yi biyayya sosai ga Ubangiji Allahnku.”
Et ceux qui demeurent au loin viendront et travailleront aussi à réédifier le temple du Seigneur; et vous saurez que le Seigneur tout-puissant M'a envoyé près de vous; et ces choses arriveront si vous êtes dociles à la voix du Seigneur votre Dieu.

< Zakariya 6 >