< Zakariya 6 >

1 Na sāke ɗaga kai sama, sai ga kekunan yaƙi guda huɗu a gabana suna fitowa tsakanin duwatsu guda biyu, duwatsun tagulla!
De nouveau, je levai les yeux pour regarder, et voici que quatre chars sortaient d’entre les deux montagnes; or, ces montagnes étaient des montagnes d’airain.
2 Karusa ta farko tana da jajjayen dawakai, ta biyu kuma baƙaƙen dawakai,
Au premier char il y avait des chevaux roux, au second char des chevaux noirs;
3 ta ukun farare dawakai, ta huɗu kuma dawakai masu ɗigo-ɗigo a dukan jikinsu, dukansu kuwa ƙarfafa.
au troisième char des chevaux blancs et au quatrième char des chevaux tachetés brun.
4 Sai na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
Je pris la parole et dis à l’ange qui conversait avec moi: "Que représentent ceux-là, seigneur?"
5 Mala’ikan ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ruhohi huɗu na sama, waɗanda suka fito daga wurin Ubangiji na dukan duniya.
L’Ange répliqua en me disant: "Ce sont les quatre vents du ciel qui sortent, après s’être présentés devant le Maître de toute la terre."
6 Wannan mai baƙaƙen dawakai zai nufi wajen ƙasar arewa, mai fararen dawakai zai nufi wajen yamma, sai kuma mai dawakai masu ɗigo-ɗigo a jiki zai nufi wajen kudu.”
Pour ce qui est du char où sont les chevaux noirs, ils prirent leur course vers le pays du Nord, les blancs suivirent leurs traces; quant aux tachetés, ils s’en allèrent vers le pays du Sud.
7 Da ƙarfafa dawakan suka fito, sai suka yi marmari su ratsa dukan duniya. Sai ya ce, “Ku ratsa dukan duniya!” Saboda haka suka ratsa dukan duniya.
Et les bruns sortirent à leur tour, demandant à aller parcourir la terre. Et il dit: "Allez et parcourez la terre!" Et ils se mirent à parcourir la terre.
8 Sai ya kira ni ya ce, “Duba, waɗanda suka nufi wajen ƙasar arewa sun ba wa Ruhuna hutu a ƙasar arewa.”
Puis, il m’apostropha et me parla en ces termes: "Vois, ceux qui s’en vont vers le pays du Nord, apaisent mon esprit dans le pays du Nord."
9 Maganar Ubangiji ta zo mini, ta ce,
La parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
10 “Ka karɓi azurfa da zinariya daga masu zaman bauta Heldai, Tobiya, Yedahiya, waɗanda suka iso daga Babilon. A ranar kuma ka je gidan Yosiya ɗan Zefaniya.
"Accepte de la part de ceux qui sont en exil les dons apportés par Heldaï, Tobia et Jedaïa et va, ce même jour, te rendre dans la maison de Josia, fils de Cefania, où ils sont arrivés de Babylone.
11 Ka ɗauki azurfar da zinariyar ka yi rawani, ka ɗora shi a kan babban firist, Yoshuwa ɗan Yehozadak.
Tu prendras de l’argent et de l’or, tu en feras des couronnes, que tu poseras sur la tête de Josué, fils de Joçadak, le grand-prêtre.
12 Ka ce masa ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ga mutumin da sunansa ne Reshe, zai kuma ratse daga inda yake yă gina haikalin Ubangiji.
Et tu lui diras ces mots: Ainsi parle l’Eternel-Cebaot: Voici un homme dont le nom est "Rejeton" et il germera de sa place pour bâtir le temple de l’Eternel.
13 Shi ne zai gina haikalin Ubangiji, za a kuma martaba shi da daraja, zai kuma zauna yă yi mulki a kan kursiyinsa. Zai zama firist a kan kursiyinsa. Kuma a tsakanin biyun za a sami zaman lafiya.’
Oui, c’est lui qui bâtira le temple de l’Eternel, il en retirera de la gloire et il s’asseoira et règnera sur son trône; un prêtre sera près de son trône, et il y aura une entente pacifique entre eux.
14 Za a ba Heldai, Tobiya, Yedahiya da kuma Hen ɗan Zefaniya kamar abin tunawa a cikin haikalin Ubangiji.
Les couronnes seront conservées dans le temple de l’Eternel, comme mémorial à l’intention de Hèlem, Tobia et Jedaïa, et comme signe d’honneur pour le fils de Cefania.
15 Waɗanda suke nesa za su zo su taimaka gina haikalin Ubangiji, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku. Wannan zai faru in kuka yi biyayya sosai ga Ubangiji Allahnku.”
Et on viendra de loin pour prendre part à la construction du temple de l’Eternel, et vous reconnaîtrez que c’est l’Eternel-Cebaot qui m’a délégué auprès de vous. Cela s’accomplira, si vous obéissez ponctuellement à la voix de l’Eternel, votre Dieu."

< Zakariya 6 >