< Zakariya 6 >

1 Na sāke ɗaga kai sama, sai ga kekunan yaƙi guda huɗu a gabana suna fitowa tsakanin duwatsu guda biyu, duwatsun tagulla!
And I lifted up mine eyes again, and looked, and, behold, there came four chariots out from between two mountains; and the mountains were mountains of brass.
2 Karusa ta farko tana da jajjayen dawakai, ta biyu kuma baƙaƙen dawakai,
In the first chariot were red horses; and in the second chariot, black horses;
3 ta ukun farare dawakai, ta huɗu kuma dawakai masu ɗigo-ɗigo a dukan jikinsu, dukansu kuwa ƙarfafa.
and in the third chariot, white horses; and in the fourth chariot, spotted-red horses.
4 Sai na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
Then I spake, and said to the angel that talked with me, What are these, my lord?
5 Mala’ikan ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ruhohi huɗu na sama, waɗanda suka fito daga wurin Ubangiji na dukan duniya.
And the angel answered and said to me, These are the four Winds of heaven, which go forth from standing before the Lord of all the earth.
6 Wannan mai baƙaƙen dawakai zai nufi wajen ƙasar arewa, mai fararen dawakai zai nufi wajen yamma, sai kuma mai dawakai masu ɗigo-ɗigo a jiki zai nufi wajen kudu.”
The black horses, which are thereto, go forth into the north country, and the white go forth after them; and the spotted go forth into the south country.
7 Da ƙarfafa dawakan suka fito, sai suka yi marmari su ratsa dukan duniya. Sai ya ce, “Ku ratsa dukan duniya!” Saboda haka suka ratsa dukan duniya.
And the red ones went forth, and sought to go, even to walk to and fro through the earth. And he said, Go, walk ye to and fro through the earth! So they walked to and fro through the earth.
8 Sai ya kira ni ya ce, “Duba, waɗanda suka nufi wajen ƙasar arewa sun ba wa Ruhuna hutu a ƙasar arewa.”
Then he cried to me, and spake to me, saying, Behold, these that go forth toward the land of the North shall execute my wrath against the land of the North.
9 Maganar Ubangiji ta zo mini, ta ce,
And the word of Jehovah came to me, saying:
10 “Ka karɓi azurfa da zinariya daga masu zaman bauta Heldai, Tobiya, Yedahiya, waɗanda suka iso daga Babilon. A ranar kuma ka je gidan Yosiya ɗan Zefaniya.
Take from those of the captivity, from Heldai, from Tobijah, and from Jedaiah, and come thou the same day, and go into the house of Josiah, the son of Zephaniah, whither they are come from Babylon;
11 Ka ɗauki azurfar da zinariyar ka yi rawani, ka ɗora shi a kan babban firist, Yoshuwa ɗan Yehozadak.
take from them silver and gold, and make a crown, and set it upon the head of Joshua, the son of Josedech, the high-priest,
12 Ka ce masa ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ga mutumin da sunansa ne Reshe, zai kuma ratse daga inda yake yă gina haikalin Ubangiji.
and speak to him, saying, Thus saith Jehovah of hosts: — Behold a man whose name is the Branch, He shall spring up from his place, And he shall build the temple of Jehovah.
13 Shi ne zai gina haikalin Ubangiji, za a kuma martaba shi da daraja, zai kuma zauna yă yi mulki a kan kursiyinsa. Zai zama firist a kan kursiyinsa. Kuma a tsakanin biyun za a sami zaman lafiya.’
He shall build the temple of Jehovah, And he shall bear the majesty, And sit and rule upon his throne, And be a priest upon his throne, And the counsel of peace shall be between them both.
14 Za a ba Heldai, Tobiya, Yedahiya da kuma Hen ɗan Zefaniya kamar abin tunawa a cikin haikalin Ubangiji.
And the crown shall be to Helem, and to Tobijah, and to Jedaiah, and to Hen, the son of Zephaniah, for a memorial in the temple of Jehovah.
15 Waɗanda suke nesa za su zo su taimaka gina haikalin Ubangiji, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku. Wannan zai faru in kuka yi biyayya sosai ga Ubangiji Allahnku.”
And they that are far off shall come and build in the temple of Jehovah; and ye shall know that Jehovah of hosts hath sent me to you. And this shall come to pass, if ye will diligently obey the voice of Jehovah, your God.

< Zakariya 6 >