< Zakariya 6 >

1 Na sāke ɗaga kai sama, sai ga kekunan yaƙi guda huɗu a gabana suna fitowa tsakanin duwatsu guda biyu, duwatsun tagulla!
Atter løftede jeg mine Øjne og skuede, og se, fire Vogne kom frem mellem de to Bjerge, og Bjergene var af Kobber.
2 Karusa ta farko tana da jajjayen dawakai, ta biyu kuma baƙaƙen dawakai,
For den første Vogn var der røde Heste, for den anden sorte,
3 ta ukun farare dawakai, ta huɗu kuma dawakai masu ɗigo-ɗigo a dukan jikinsu, dukansu kuwa ƙarfafa.
for den tredje hvide og for den fjerde brogede.
4 Sai na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
Jeg spurgte Engelen, som talte med mig: "Hvad betyder disse Herre?"
5 Mala’ikan ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ruhohi huɗu na sama, waɗanda suka fito daga wurin Ubangiji na dukan duniya.
Og Engelen svarede: "Det er Himmelens fire Vinde, som drager ud efter at have fremstillet sig for al Jordens Herre.
6 Wannan mai baƙaƙen dawakai zai nufi wajen ƙasar arewa, mai fararen dawakai zai nufi wajen yamma, sai kuma mai dawakai masu ɗigo-ɗigo a jiki zai nufi wajen kudu.”
Vognen med de sorte Heste for drager ud til Nordlandet, de hvide til Østlandet og de brogede til Sydlandet;
7 Da ƙarfafa dawakan suka fito, sai suka yi marmari su ratsa dukan duniya. Sai ya ce, “Ku ratsa dukan duniya!” Saboda haka suka ratsa dukan duniya.
de røde drager mod Vest. Og de var ivrige efter at komme af Sted for at drage ud over Jorden. Da sagde han: "Af Sted; drag ud over Jorden!" Og de drog ud over Jorden.
8 Sai ya kira ni ya ce, “Duba, waɗanda suka nufi wajen ƙasar arewa sun ba wa Ruhuna hutu a ƙasar arewa.”
Så kaldte han på mig og talte således til mig: "Se, de, som drager ud til Nordlandet, lader min Ånd dale ned over Nordens Land."
9 Maganar Ubangiji ta zo mini, ta ce,
HERRENs Ord kom til mig således:
10 “Ka karɓi azurfa da zinariya daga masu zaman bauta Heldai, Tobiya, Yedahiya, waɗanda suka iso daga Babilon. A ranar kuma ka je gidan Yosiya ɗan Zefaniya.
Tag imod Gaver fra de landflygtige, fra Heldaj, Tobija og Jedaja; endnu i Dag skal du gå indtil Josjija, Zefanjas Søn, som er kommet fra Babel,
11 Ka ɗauki azurfar da zinariyar ka yi rawani, ka ɗora shi a kan babban firist, Yoshuwa ɗan Yehozadak.
og modtage Sølv og Guld. Lad så lave en Krone og sæt den på Josuas Hoved
12 Ka ce masa ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ga mutumin da sunansa ne Reshe, zai kuma ratse daga inda yake yă gina haikalin Ubangiji.
med de Ord: "Så siger Hærskarers HERRE: Se, der kommer en Mand, hvis Navn er Zemak under ham skal det spire, og han skal bygge HERRENs Helligdom.
13 Shi ne zai gina haikalin Ubangiji, za a kuma martaba shi da daraja, zai kuma zauna yă yi mulki a kan kursiyinsa. Zai zama firist a kan kursiyinsa. Kuma a tsakanin biyun za a sami zaman lafiya.’
Han skal bygge HERRENs Helligdom, og han skal vinde Højhed og sidde som Hersker på sin Trone: og han skal være Præst ved hans højre Side, og der skal være fuld Enighed mellem de to.
14 Za a ba Heldai, Tobiya, Yedahiya da kuma Hen ɗan Zefaniya kamar abin tunawa a cikin haikalin Ubangiji.
Men Kronen skal blive i HERRENs Helligdom til Minde om Heldaj, Tobija, Jedaja og Hen, Zefanjas Søn.
15 Waɗanda suke nesa za su zo su taimaka gina haikalin Ubangiji, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku. Wannan zai faru in kuka yi biyayya sosai ga Ubangiji Allahnku.”
Langvejs fra skal man komme og bygge på HERRENs Helligdom; og I skal kende, at Hærskarers HERRE har sendt mig til eder. Og dersom I adlyder HERREN eders Gud - - -

< Zakariya 6 >