< Zakariya 5 >

1 Na sāke dubawa sai ga naɗaɗɗen littafi mai firiya a gabana!
Puis je me retournai, et levai mes yeux pour regarder; et voici un rouleau volant.
2 Sai ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Sai na amsa na ce, “Na ga naɗaɗɗen littafi mai firiya, tsawonsa ƙafa talatin da fāɗinsa kuma ƙafa goma sha biyar.”
Alors il me dit: Que vois-tu? Et je répondis: Je vois un rouleau volant, dont la longueur est de vingt coudées, et sa largeur de dix coudées.
3 Sai ya ce mini, “Wannan ce la’anar da za tă ratsa dukan ƙasar; gama bisa ga abin da ya ce a gefe ɗaya, za a kawar da kowane ɓarawo, kuma bisa ga abin da ya ce a ɗaya gefen za a kawar da duk mai rantsuwar ƙarya.
Et il me dit: C'est là l'exécration du serment qui sort sur le dessus de toute la terre; car quiconque d'entre ce [peuple-ci] dérobe, sera puni comme elle; et quiconque d'entre ce [peuple]-ci jure, sera puni comme elle.
4 Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan aika shi, zai shiga gidan ɓarawo, da gidan mai rantsuwar ƙarya da sunana. Zai kasance a gidansa yă hallaka gidan da katakon da duwatsun.’”
Je déploierai cette exécration, dit l'Eternel des armées, et elle entrera dans la maison du larron, et dans la maison de celui qui jure [faussement] par mon Nom, et elle logera au milieu de leur maison, et la consumera avec son bois et ses pierres.
5 Sai mala’ikan da yake mini magana ya zo gaba ya ce mini, “Duba ka gani ko mene ne wannan da yake fitowa.”
Et l'Ange qui parlait avec moi sortit, et me dit: Lève maintenant tes yeux, et regarde ce qui sort.
6 Na tambaya na ce, “Mene ne?” Ya amsa ya ce, “Kwando ne na awo.” Ya ƙara da cewa, “Wannan shi ne laifin mutanen a duk fāɗin ƙasar.”
Et je dis: Qu'est-ce? Et il [répondit]: C'est un Epha qui sort dehors. Puis il dit: C'est l'œil que j'ai sur eux par toute la terre.
7 Sa’an nan aka ɗaga murfin dalman, a ciki kuwa ga mace zaune!
Et voici, on portait une masse de plomb, et une femme était assise au milieu de l'Epha.
8 Ya ce, “Wannan mugunta ce,” ya kuma tura ta cikin kwandon ya rufe da murfin dalman, ya kuma danna da dutse.
Et il dit: C'est là la méchanceté; puis il la jeta au milieu de l'Epha, et mit la masse de plomb sur son ouverture.
9 Na ɗaga idona sama, sai ga mata biyu a gabana, iska tana hura fikafikansu! Suna da fikafikai kamar na shamuwa, suka kuma ɗaga kwandon sama.
Puis levant mes yeux, je regardai, et voici deux femmes qui sortaient, et le vent soufflait dans leurs ailes; or elles avaient des ailes comme les ailes d'une cigogne; et elles enlevèrent l'Epha entre la terre et les cieux.
10 Na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Ina za ku kai kwandon?”
Et je dis à l'Ange qui parlait avec moi: Où emportent-elles l'Epha?
11 Ya amsa ya ce, “Zuwa ƙasar Babiloniya don a gina masa haikali. Sa’ad da aka gama ginin, za a ajiye shi a ciki.”
Et il me répondit: C'est pour lui bâtir une maison au pays de Sinhar laquelle étant établie, il sera là posé sur sa base.

< Zakariya 5 >