< Zakariya 5 >
1 Na sāke dubawa sai ga naɗaɗɗen littafi mai firiya a gabana!
Puis, je me repris à lever les yeux et je regardai: c’était un rouleau qui volait.
2 Sai ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Sai na amsa na ce, “Na ga naɗaɗɗen littafi mai firiya, tsawonsa ƙafa talatin da fāɗinsa kuma ƙafa goma sha biyar.”
Il me dit: "Que vois-tu?" Je répondis: "Je vois un rouleau qui vole; sa longueur est de vingt coudées et sa largeur de dix coudées."
3 Sai ya ce mini, “Wannan ce la’anar da za tă ratsa dukan ƙasar; gama bisa ga abin da ya ce a gefe ɗaya, za a kawar da kowane ɓarawo, kuma bisa ga abin da ya ce a ɗaya gefen za a kawar da duk mai rantsuwar ƙarya.
Il me dit: "C’Est là la malédiction qui se répand sur la face de tout ce pays; car quiconque dérobe sera rejeté d’ici comme elle l’annonce, et quiconque se parjure sera rejeté d’ici comme elle l’annonce.
4 Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan aika shi, zai shiga gidan ɓarawo, da gidan mai rantsuwar ƙarya da sunana. Zai kasance a gidansa yă hallaka gidan da katakon da duwatsun.’”
Je lui ai donné libre cours, dit l’Eternel-Cebaot, pour qu’elle entre dans la maison du larron et dans la maison de celui qui jure faussement par mon nom: elle élira domicile au milieu de sa maison et la ruinera avec sa charpente et ses pierres."
5 Sai mala’ikan da yake mini magana ya zo gaba ya ce mini, “Duba ka gani ko mene ne wannan da yake fitowa.”
Puis l’ange qui conversait avec moi sortit et me dit: "Lève donc les yeux et regarde ce qui apparaît-là."
6 Na tambaya na ce, “Mene ne?” Ya amsa ya ce, “Kwando ne na awo.” Ya ƙara da cewa, “Wannan shi ne laifin mutanen a duk fāɗin ƙasar.”
Et je dis: "Qu’est-ce?" II répondit: "C’Est l’êpha qui apparaît." Et il ajouta: "C’Est vers elle que se portent les regards sur toute la terre."
7 Sa’an nan aka ɗaga murfin dalman, a ciki kuwa ga mace zaune!
Or, voici qu’un bloc de plomb était soulevé et qu’on voyait une femme assise dans l’êpha.
8 Ya ce, “Wannan mugunta ce,” ya kuma tura ta cikin kwandon ya rufe da murfin dalman, ya kuma danna da dutse.
Il dit: "C’Est là la Méchanceté!" Il la repoussa au fond de l’êpha et rejeta la masse de plomb sur l’ouverture.
9 Na ɗaga idona sama, sai ga mata biyu a gabana, iska tana hura fikafikansu! Suna da fikafikai kamar na shamuwa, suka kuma ɗaga kwandon sama.
Je levai les yeux et je vis sortir deux femmes, les ailes gonflées par le vent. Elles avaient, en effet, des ailes pareilles aux ailes de la cigogne, et elles transportèrent l’êpha entre ciel et terre.
10 Na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Ina za ku kai kwandon?”
Je dis à l’ange, qui conversait avec moi: "Où transportent-elles l’êpha?"
11 Ya amsa ya ce, “Zuwa ƙasar Babiloniya don a gina masa haikali. Sa’ad da aka gama ginin, za a ajiye shi a ciki.”
Il me répondit: " Elles vont pour lui bâtir une demeure dans le pays de Sennaar, et quand celle-ci sera solidement établie, elle y sera déposée à demeure fixe."