< Zakariya 5 >

1 Na sāke dubawa sai ga naɗaɗɗen littafi mai firiya a gabana!
Je levai de nouveau les yeux et je vis: Et voici un rouleauqui volait.
2 Sai ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Sai na amsa na ce, “Na ga naɗaɗɗen littafi mai firiya, tsawonsa ƙafa talatin da fāɗinsa kuma ƙafa goma sha biyar.”
Il me dit: « Que vois-tu? » Je dis: « Je vois un rouleau qui vole; sa longueur est de vingt coudées et sa largeur de dix coudées. »
3 Sai ya ce mini, “Wannan ce la’anar da za tă ratsa dukan ƙasar; gama bisa ga abin da ya ce a gefe ɗaya, za a kawar da kowane ɓarawo, kuma bisa ga abin da ya ce a ɗaya gefen za a kawar da duk mai rantsuwar ƙarya.
Et il me dit: C’est la malédiction qui sort sur la face de tout le pays; car, selon ce qui y est écrit, quiconque dérobe sera balayé d’ici, et, selon ce qui y est écrit, quiconque jure sera balayé d’ici.
4 Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan aika shi, zai shiga gidan ɓarawo, da gidan mai rantsuwar ƙarya da sunana. Zai kasance a gidansa yă hallaka gidan da katakon da duwatsun.’”
Je l’ai déchaînée, — oracle de Yahweh des armées, — et elle arrivera à la maison du voleur et à la maison de celui qui jure par mon nom en mentant; elle se logera au milieu de sa maison et la consumera, le bois et les pierres.
5 Sai mala’ikan da yake mini magana ya zo gaba ya ce mini, “Duba ka gani ko mene ne wannan da yake fitowa.”
L’ange qui parlait avec moi parut et me dit: « Lève les yeux et regarde ce qui apparaît. » Je dis: « Qu’est-ce? »
6 Na tambaya na ce, “Mene ne?” Ya amsa ya ce, “Kwando ne na awo.” Ya ƙara da cewa, “Wannan shi ne laifin mutanen a duk fāɗin ƙasar.”
Il dit: « C’est l’épha qui apparaît ». Et il ajouta: « C’est à cela que s’attache leur regard dans tout le pays. »
7 Sa’an nan aka ɗaga murfin dalman, a ciki kuwa ga mace zaune!
Et voici qu’un disque de plomb fut soulevé, et il y avait une femme assise au milieu de l’épha.
8 Ya ce, “Wannan mugunta ce,” ya kuma tura ta cikin kwandon ya rufe da murfin dalman, ya kuma danna da dutse.
Il dit: « Cette femme est l’improbité. » Et il la repoussa au milieu de l’épha et jeta sur l’ouverture de celui-ci la masse de plomb.
9 Na ɗaga idona sama, sai ga mata biyu a gabana, iska tana hura fikafikansu! Suna da fikafikai kamar na shamuwa, suka kuma ɗaga kwandon sama.
Et je levai les yeux, et je vis. Et voici que deux femmes apparurent; du vent soufflait dans leurs ailes; elles avaient des ailes pareilles aux ailes de la cigogne. Et elles enlevèrent l’épha entre le ciel et la terre.
10 Na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Ina za ku kai kwandon?”
Je dis à l’ange qui parlait avec moi: « Où emportent-elles l’épha? »
11 Ya amsa ya ce, “Zuwa ƙasar Babiloniya don a gina masa haikali. Sa’ad da aka gama ginin, za a ajiye shi a ciki.”
Il me répondit: « Elles l’emportent pour lui bâtir une maison au pays de Sennaar; et, quand elle aura été fondée, on le placera là en son lieu.

< Zakariya 5 >