< Zakariya 5 >

1 Na sāke dubawa sai ga naɗaɗɗen littafi mai firiya a gabana!
Then again I lifted up mine eyes, and saw, and behold, a flying roll.
2 Sai ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Sai na amsa na ce, “Na ga naɗaɗɗen littafi mai firiya, tsawonsa ƙafa talatin da fāɗinsa kuma ƙafa goma sha biyar.”
And he said unto me, What seest thou? And I answered, I see a flying roll; the length thereof is twenty cubits, and the breadth thereof ten cubits.
3 Sai ya ce mini, “Wannan ce la’anar da za tă ratsa dukan ƙasar; gama bisa ga abin da ya ce a gefe ɗaya, za a kawar da kowane ɓarawo, kuma bisa ga abin da ya ce a ɗaya gefen za a kawar da duk mai rantsuwar ƙarya.
Then said he unto me, This is the curse that goeth forth over the face of the whole land: for every one that stealeth shall be purged out on the one side according to it; and every one that sweareth shall be purged out on the other side according to it.
4 Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan aika shi, zai shiga gidan ɓarawo, da gidan mai rantsuwar ƙarya da sunana. Zai kasance a gidansa yă hallaka gidan da katakon da duwatsun.’”
I will cause it to go forth, saith the LORD of hosts, and it shall enter into the house of the thief, and into the house of him that sweareth falsely by my name: and it shall abide in the midst of his house, and shall consume it with the timber thereof and the stones thereof.
5 Sai mala’ikan da yake mini magana ya zo gaba ya ce mini, “Duba ka gani ko mene ne wannan da yake fitowa.”
Then the angel that talked with me went forth, and said unto me, Lift up now thine eyes, and see what is this that goeth forth.
6 Na tambaya na ce, “Mene ne?” Ya amsa ya ce, “Kwando ne na awo.” Ya ƙara da cewa, “Wannan shi ne laifin mutanen a duk fāɗin ƙasar.”
And I said, What is it? And he said, This is the ephah that goeth forth. He said moreover, This is their resemblance in all the land:
7 Sa’an nan aka ɗaga murfin dalman, a ciki kuwa ga mace zaune!
(and behold, there was lifted up a talent of lead: ) and this is a woman sitting in the midst of the ephah.
8 Ya ce, “Wannan mugunta ce,” ya kuma tura ta cikin kwandon ya rufe da murfin dalman, ya kuma danna da dutse.
And he said, This is Wickedness; and he cast her down into the midst of the ephah: and he cast the weight of lead upon the mouth thereof.
9 Na ɗaga idona sama, sai ga mata biyu a gabana, iska tana hura fikafikansu! Suna da fikafikai kamar na shamuwa, suka kuma ɗaga kwandon sama.
Then lifted I up mine eyes, and saw, and behold, there came forth two women, and the wind was in their wings; now they had wings like the wings of a stork: and they lifted up the ephah between the earth and the heaven.
10 Na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Ina za ku kai kwandon?”
Then said I to the angel that talked with me, Whither do these bear the ephah?
11 Ya amsa ya ce, “Zuwa ƙasar Babiloniya don a gina masa haikali. Sa’ad da aka gama ginin, za a ajiye shi a ciki.”
And he said unto me, To build her an house in the land of Shinar: and when it is prepared, she shall be set there in her own place.

< Zakariya 5 >