< Zakariya 5 >

1 Na sāke dubawa sai ga naɗaɗɗen littafi mai firiya a gabana!
And I turn back, and lift up my eyes, and look, and behold, a flying scroll.
2 Sai ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Sai na amsa na ce, “Na ga naɗaɗɗen littafi mai firiya, tsawonsa ƙafa talatin da fāɗinsa kuma ƙafa goma sha biyar.”
And he says to me, “What are you seeing?” And I say, “I am seeing a flying scroll, its length [is] twenty by the cubit, and its breadth [is] ten by the cubit.”
3 Sai ya ce mini, “Wannan ce la’anar da za tă ratsa dukan ƙasar; gama bisa ga abin da ya ce a gefe ɗaya, za a kawar da kowane ɓarawo, kuma bisa ga abin da ya ce a ɗaya gefen za a kawar da duk mai rantsuwar ƙarya.
And he says to me, “This [is] the execration that is going forth over the face of all the land, for everyone who is stealing, on the one side, according to it, has been declared innocent, and everyone who has sworn, on the other side, according to it, has been declared innocent.”
4 Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan aika shi, zai shiga gidan ɓarawo, da gidan mai rantsuwar ƙarya da sunana. Zai kasance a gidansa yă hallaka gidan da katakon da duwatsun.’”
“I have brought it out,” a declaration of YHWH of Hosts, “and it has come into the house of the thief, and into the house of him who has sworn in My Name with a falsehood, and it has remained in the midst of his house, and has consumed it, both its wood and its stones.”
5 Sai mala’ikan da yake mini magana ya zo gaba ya ce mini, “Duba ka gani ko mene ne wannan da yake fitowa.”
And the messenger who is speaking with me goes forth and says to me, “Now lift up your eyes, and [do you] see what this [is] that is coming forth?”
6 Na tambaya na ce, “Mene ne?” Ya amsa ya ce, “Kwando ne na awo.” Ya ƙara da cewa, “Wannan shi ne laifin mutanen a duk fāɗin ƙasar.”
And I say, “What [is] it?” And he says, “This—the ephah that is coming forth.” And he says, “This [is] their aspect in all the land.
7 Sa’an nan aka ɗaga murfin dalman, a ciki kuwa ga mace zaune!
And behold, a disc of lead lifted up; and this [is] a woman sitting in the midst of the ephah.”
8 Ya ce, “Wannan mugunta ce,” ya kuma tura ta cikin kwandon ya rufe da murfin dalman, ya kuma danna da dutse.
And he says, “This [is] the wicked woman.” And he casts her into the midst of the ephah, and casts the weight of lead on its mouth.
9 Na ɗaga idona sama, sai ga mata biyu a gabana, iska tana hura fikafikansu! Suna da fikafikai kamar na shamuwa, suka kuma ɗaga kwandon sama.
And I lift up my eyes, and see, and behold, two women are coming forth, and wind [is] in their wings; and they have wings like wings of the stork, and they lift up the ephah between the earth and the heavens.
10 Na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Ina za ku kai kwandon?”
And I say to the messenger who is speaking with me, “To where [are] they causing the ephah to go?”
11 Ya amsa ya ce, “Zuwa ƙasar Babiloniya don a gina masa haikali. Sa’ad da aka gama ginin, za a ajiye shi a ciki.”
And he says to me, “To build a house for it in the land of Shinar.” And it has been prepared and has been placed there on its base.

< Zakariya 5 >