< Zakariya 5 >

1 Na sāke dubawa sai ga naɗaɗɗen littafi mai firiya a gabana!
And I again lifted up my eyes, and looked, and behold there was a flying roll[-book].
2 Sai ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Sai na amsa na ce, “Na ga naɗaɗɗen littafi mai firiya, tsawonsa ƙafa talatin da fāɗinsa kuma ƙafa goma sha biyar.”
And he said unto me, What seest thou? And I answered, I see a flying roll, its length is twenty cubits, and its breadth ten cubits.
3 Sai ya ce mini, “Wannan ce la’anar da za tă ratsa dukan ƙasar; gama bisa ga abin da ya ce a gefe ɗaya, za a kawar da kowane ɓarawo, kuma bisa ga abin da ya ce a ɗaya gefen za a kawar da duk mai rantsuwar ƙarya.
Then said he unto me, This is the curse that goeth forth over the face of all the earth; for every one that stealeth as it is on this side shall be in an equal degree entirely destroyed, as also every one that sweareth [falsely] as it is on that side shall be likewise entirely destroyed.
4 Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan aika shi, zai shiga gidan ɓarawo, da gidan mai rantsuwar ƙarya da sunana. Zai kasance a gidansa yă hallaka gidan da katakon da duwatsun.’”
I bring it forth, saith the Lord of hosts, and it shall enter into the house of the thief, and into the house of him that sweareth falsely by my name: and it shall remain in the midst of his house, and shall consume it with its timber and its stones.
5 Sai mala’ikan da yake mini magana ya zo gaba ya ce mini, “Duba ka gani ko mene ne wannan da yake fitowa.”
Then went forth the angel that spoke with me, and said unto me, Do but lift up thy eyes, and see what is this that goeth forth.
6 Na tambaya na ce, “Mene ne?” Ya amsa ya ce, “Kwando ne na awo.” Ya ƙara da cewa, “Wannan shi ne laifin mutanen a duk fāɗin ƙasar.”
And I said, What is it? And he said, This is an ephah that goeth forth. He said moreover, This is their appearance through all the earth.
7 Sa’an nan aka ɗaga murfin dalman, a ciki kuwa ga mace zaune!
And, behold, there was lifted up a heavy [cover] of lead: and there was a certain woman sitting in the midst of the ephah.
8 Ya ce, “Wannan mugunta ce,” ya kuma tura ta cikin kwandon ya rufe da murfin dalman, ya kuma danna da dutse.
And he said, This is the wickedness. And he cast her into the midst of the ephah; and he cast the weighty lead cover upon the mouth thereof.
9 Na ɗaga idona sama, sai ga mata biyu a gabana, iska tana hura fikafikansu! Suna da fikafikai kamar na shamuwa, suka kuma ɗaga kwandon sama.
Then did I lift up my eyes, and looked, and, behold, there came out two women, having the wind in their wings, and they had wings like the wings of a stork: and they lifted up the ephah between the earth and the heaven.
10 Na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Ina za ku kai kwandon?”
Then said I to the angel that spoke with me, Whither are these bearing away the ephah?
11 Ya amsa ya ce, “Zuwa ƙasar Babiloniya don a gina masa haikali. Sa’ad da aka gama ginin, za a ajiye shi a ciki.”
And he said unto me, To build for it a house in the land of Shin'ar: and when this is erected, then will the other be set there upon its own base.

< Zakariya 5 >