< Zakariya 4 >

1 Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
O anjo que falou comigo veio novamente e me despertou, como um homem que é despertado de seu sono.
2 Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
Ele me disse: “O que você vê?”. Eu disse: “Eu vi, e eis que uma lâmpada está toda de ouro, com sua tigela em cima, e suas sete lâmpadas em cima; há sete tubos para cada uma das lâmpadas que estão em cima dela;
3 Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
e duas oliveiras ao lado dela, uma do lado direito da tigela, e outra do lado esquerdo dela”.
4 Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
Eu respondi e falei com o anjo que falou comigo, dizendo: “O que é isto, meu senhor”?
5 Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
Então o anjo que falou comigo me respondeu: “Você não sabe o que é isso?”. Eu disse: “Não, meu senhor”.
6 Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Então ele respondeu e falou comigo, dizendo: “Esta é a palavra de Javé para Zerubbabel, dizendo: 'Não pelo poder, nem pelo poder, mas pelo meu Espírito', diz Javé dos Exércitos.
7 “Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
Quem é você, grande montanha? Antes de Zorobabel você é uma planície; e ele fará sair a pedra de toque com gritos de 'Graça, graça, a ela'”.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
Além disso, a palavra de Javé veio até mim, dizendo:
9 “Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
“As mãos de Zerubbabel lançaram os alicerces desta casa. Suas mãos também a terminarão; e você saberá que Javé dos Exércitos me enviou a você”.
10 “Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
De fato, quem despreza o dia das pequenas coisas? Pois estes sete se alegrarão, e verão a linha de prumo na mão de Zerubabel. Estes são os olhos de Javé, que correm para frente e para trás em toda a terra”.
11 Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
Depois perguntei-lhe: “O que são estas duas oliveiras no lado direito da bancada e no lado esquerdo da mesma”?
12 Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
Perguntei-lhe pela segunda vez: “O que são esses dois ramos de oliveira, que estão ao lado dos dois bicos dourados que derramam o óleo dourado de si mesmos?
13 Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
Ele me respondeu: “Você não sabe o que é isso?” Eu disse: “Não, meu senhor”.
14 Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”
Então ele disse: “Estes são os dois ungidos que estão ao lado do Senhor de toda a terra”.

< Zakariya 4 >