< Zakariya 4 >

1 Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
و فرشته‌ای که با من تکلم می‌نمود، برگشته، مرا مثل شخصی که از خواب بیدار شودبیدار کرد،۱
2 Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
و به من گفت: «چه چیز می‌بینی؟» گفتم: «نظر کردم و اینک شمعدانی که تمامش طلاست و روغندانش بر سرش و هفت چراغش بر آن است و هر چراغ که بر سرش می‌باشد هفت لوله دارد.۲
3 Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
و به پهلوی آن دو درخت زیتون که یکی بطرف راست روغندان و دیگری بطرف چپش می‌باشد.»۳
4 Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
و من توجه نموده، فرشته‌ای را که با من تکلم می‌نمود خطاب کرده، گفتم: «ای آقایم اینها چه می‌باشد؟»۴
5 Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
و فرشته‌ای که با من تکلم می‌نمودمرا جواب داد و گفت: «آیا نمی دانی که اینهاچیست؟» گفتم: «نه‌ای آقایم.»۵
6 Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
او در جواب من گفت: «این است کلامی که خداوند به زربابل می‌گوید: نه به قدرت و نه به قوت بلکه به روح من. قول یهوه صبایوت این است.۶
7 “Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
‌ای کوه بزرگ تو چیستی؟ در حضورزربابل به همواری مبدل خواهی شد و سنگ سرآن را بیرون خواهد آورد و صدا خواهند زد فیض فیض بر آن باشد.»۷
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
و کلام خداوند بر من نازل شده، گفت:۸
9 “Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
«دستهای زربابل این خانه را بنیاد نهاد و دستهای وی آن را تمام خواهد کرد و خواهی دانست که یهوه صبایوت مرا نزد شما فرستاده است.۹
10 “Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
زیرا کیست که روز امور کوچک را خوار شمارد زیراکه این هفت مسرور خواهند شد حینی که شاغول را در دست زربابل می‌بینند. و اینها چشمان خداوند هستند که در تمامی جهان ترددمی نمایند.»۱۰
11 Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
پس من او را خطاب کرده، گفتم: «این دودرخت زیتون که بطرف راست و بطرف چپ شمعدان هستند چه می‌باشند؟»۱۱
12 Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
و بار دیگر او را خطاب کرده، گفتم که «این دو شاخه زیتون به پهلوی دو لوله زرینی که روغن طلا را از خود می‌ریزد چیستند؟»۱۲
13 Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
او مرا جواب داده، گفت: «آیا نمی دانی که اینها چیستند؟» گفتم: «نه‌ای آقایم.»۱۳
14 Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”
گفت: «اینها پسران روغن زیت می‌باشند که نزد مالک تمامی جهان می‌ایستند.»۱۴

< Zakariya 4 >