< Zakariya 4 >

1 Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
Et l’ange qui parlait en moi revint, et me réveilla comme un homme qu’on réveille de son sommeil.
2 Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
Et il me dit: Que vois-tu, toi? Et je répondis: J’ai vu, et voilà un chandelier tout d’or, et sa lampe sur son sommet, et ses sept lampes au-dessus; et sept canaux aux lampes qui étaient sur son sommet;
3 Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
Et deux oliviers au-dessus; un à la droite de la lampe, et un à sa gauche.
4 Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
Et je pris la parole, et je dis à l’ange qui parlait en moi: Qu’est ceci, mon Seigneur?
5 Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
Et l’ange qui parlait en moi me répondit et me dit: Est-ce que tu ne sais pas ce que c’est? Et je dis: Non, mon Seigneur.
6 Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Et il reprit, et s’adressa à moi, disant: Voici la parole du Seigneur à Zorobabel. Ce n’est point par une armée, ni par la force, que tu achèveras le temple, mais par mon esprit, dit le Seigneur des armées.
7 “Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
Qu’es-tu, grande montagne, devant Zorobabel? tu seras aplanie; il posera la pierre principale, et il ajoutera une beauté égale à sa beauté.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
9 “Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
Les mains de Zorobabel ont fondé cette maison, et ses mains l’achèveront; et vous saurez que le Seigneur des armées m’a envoyé vers vous.
10 “Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
Car qui a vu avec mépris les jours courts? Mais on se réjouira, et on verra le plomb à la main de Zorobabel. Ce sont là les sept yeux du Seigneur qui parcourent toute la terre.
11 Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
Et je repris et je lui dis: Que sont ces deux oliviers à la droite du chandelier, et à sa gauche?
12 Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
Et je repris une seconde fois, et je lui dis: Que sont ces deux branches d’oliviers qui sont auprès de deux becs d’or dans lesquels sont les canaux d’or par où coule l’huile?
13 Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
Et il m’interpella, en disant: Est-ce que tu ne sais pas ce que c’est? Et je répondis: Non, mon Seigneur.
14 Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”
Et il dit: Ce sont les deux fils de l’huile sainte, qui assistent devant le Dominateur de toute la terre.

< Zakariya 4 >