< Zakariya 4 >

1 Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
L’Ange qui conversait avec moi revint; il me réveilla comme un homme qu’on réveillerait de son sommeil.
2 Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
Et il me dit: "Que vois-tu?" Je répondis: "Je vois un chandelier tout en or son récipient sur son sommet, ses sept lampes alignéeset sept conduits pour les lampes qui en couronnent le sommet.
3 Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
Puis, deux oliviers à ses côtés, l’un à droite du récipient, l’autre à gauche."
4 Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
Je repris et je dis à l’ange qui conversait avec moi: "Qu’est-ce que ces choses, Seigneur?"
5 Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
L’Ange qui conversait avec moi me répondit: "Quoi! Tu ne sais donc pas ce que signifient ces choses?" Je répondis: "Non, Seigneur!"
6 Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Il reprit et me parla en ces termes: "Ceci est la parole de l’Eternel à Zorobabel: Ni par la puissance ni par la force, mais bien par mon esprit! dit l’Eternel-Cebaot.
7 “Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
Qu’es-tu, grande montagne, devant Zorobabel? une simple plaine. Qu’il amène la pierre du faîte au milieu des acclamations: "Qu’elle est belle! Qu’elle est belle!"
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
La parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
9 “Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
"Les mains de Zorobabel ont fondé cette maison, et ses mains l’achèveront, afin que tu reconnaisses que c’est l’Eternel-Cebaot qui m’a envoyé vers vous.
10 “Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
Car qui mépriserait le jour de ces humbles commencements? Plutôt se réjouiront-ils de voir la pierre du niveau dans la main de Zorobabel. Ces sept-là sont les yeux de l’Eternel qui parcourent toute la terre."
11 Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
Je pris la parole et lui dis: "Qu’est-ce que ces deux oliviers à droite et à gauche du chandelier?"
12 Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
Je repris pour la seconde fois et lui dis: "Qu’est-ce que ces deux branches d’olivier à côté des deux tuyaux d’or qui laissent couler le liquide doré?"
13 Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
Il me répondit en ces termes: "Quoi! Tu ne sais pas ce qu’elles signifient? Non, Seigneur!" répliquai-je.
14 Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”
Alors, il dit: "Ce sont les deux hommes consacrés par l’huile, qui se tiennent auprès du Maître de toute la terre!"

< Zakariya 4 >