< Zakariya 4 >

1 Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
And the aungel turnede ayen, that spak in me, and reiside me, as a man that is reisid of his sleep.
2 Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
And he seide to me, What seest thou? And Y seide, Y saiy, and lo! a candilstike al of gold, and the laumpe therof on the heed therof, and seuene lanternes therof on it, and seuene vessels for to holde oyle to the lanternes, that weren on the heed therof.
3 Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
And twei olyues there onne, oon of the riythalf `of the laumpe, and `an other on the left half therof.
4 Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
And Y answeride, and seide to the aungel that spak in me, and Y seide, What ben these thingis, my lord?
5 Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
And the aungel that spak in me, answeride, and seide to me, Whether thou woist not what ben these thingis? And Y seide, No, my lord.
6 Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And he answeride, and seide to me, and spak, This is the word of the Lord, seiynge to Sorobabel, Not in oost, nether in strengthe, but in my spirit, seith the Lord of oostis.
7 “Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
Who art thou, greet hil, bifore Sorobabel in to pleyn? and he schal lede out the firste stoon, and schal make euene grace to grace therof.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
And the word of the Lord was maad to me,
9 “Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
and seide, The hondis of Sorobabel foundiden this hous, and the hondis of hym schulen perfourme it; and ye schulen wite, that the Lord of oostis sente me to you.
10 “Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
Who forsothe dispiside litle daies? and thei schulen be glad, and schulen se a stoon of tyn in the hond of Sorobabel. These ben seuene iyen of the Lord, that rennen aboute in to al erthe.
11 Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
And Y answeride, and seide to hym, What ben these tweyne olyues on the riythalf of the candilstike, and at the lift-half therof?
12 Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
And Y answeryde the secounde tyme, and seide to hym, What ben the tweyne eeris, ether ripe fruyt, of olyues, that ben bisidis the twei bilis of gold, in whiche ben oile vesselis of gold?
13 Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
And he seide to me, and spak, Whether thou woost not what ben these thingis?
14 Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”
And Y seide, No, my lord. And he seide, These ben twei sones of oile of schynyng, whiche stonden nyy to the lordli gouernour of al erthe.

< Zakariya 4 >