< Zakariya 4 >

1 Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
Then the angel who was talking with me turned and roused me like a man roused from his sleep.
2 Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
He said to me, “What do you see?” I said, “I see a lampstand made entirely of gold, with a bowl on its top. It has seven lamps on it and seven lamp wicks at the top of each lamp.
3 Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
Two olive trees are by it, one on the right side of the bowl and the other on the left side.”
4 Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
So I spoke again to the angel who was talking with me. I said, “What do these things mean, my master?”
5 Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
The angel who was talking with me answered and said to me, “Do you not know what these things mean?” I said, “No, my master.”
6 Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
So he said to me, “This is the word of Yahweh to Zerubbabel: Not by might nor by power, but by my Spirit, says Yahweh of hosts.
7 “Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
What are you, great mountain? Before Zerubbabel you will become a plain, and he will bring out the top stone to shouts of 'Grace! Grace to it!'”
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
The word of Yahweh came to me, saying,
9 “Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
“The hands of Zerubbabel have laid the foundation of this house and his hands will bring it to completion.” Then you will know that Yahweh of hosts has sent me to you.
10 “Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
Who has despised the day of small things? These people will rejoice and will see the plumb stone in the hand of Zerubbabel. (These seven lamps are the eyes of Yahweh that roam over the whole earth.)
11 Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
Then I asked the angel, “What are these two olive trees that stand on the left and the right of the lampstand?”
12 Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
Once more I asked him, “What are these two olive branches beside the two gold pipes that have golden oil pouring out of them?”
13 Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
Then he said to me, “Do you not know what these are?” I said, “No, my master.”
14 Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”
So he said, “These are the sons of fresh olive oil who stand before the Lord of all the earth.”

< Zakariya 4 >