< Zakariya 4 >

1 Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
and to return: return [the] messenger: angel [the] to speak: speak in/on/with me and to rouse me like/as man which to rouse from sleep his
2 Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
and to say to(wards) me what? you(m. s.) to see: see (and to say *Q(K)*) to see: see and behold lampstand gold all her and bowl upon head: top her and seven lamp her upon her seven and seven casting to/for lamp which upon head: top her
3 Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
and two olive upon her one from right [the] bowl and one upon left her
4 Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
and to answer and to say to(wards) [the] messenger: angel [the] to speak: speak in/on/with me to/for to say what? these lord my
5 Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
and to answer [the] messenger: angel [the] to speak: speak in/on/with me and to say to(wards) me not to know what? they(masc.) these and to say not lord my
6 Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
and to answer and to say to(wards) me to/for to say this word LORD to(wards) Zerubbabel to/for to say not in/on/with strength and not in/on/with strength that if: except if: except in/on/with spirit my to say LORD Hosts
7 “Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
who? you(m. s.) mountain: mount [the] great: large to/for face: before Zerubbabel to/for plain and to come out: send [obj] [the] stone [the] top shout favor favor to/for her
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
and to be word LORD to(wards) me to/for to say
9 “Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
hand Zerubbabel to found [the] house: home [the] this and hand his to cut off: to end and to know for LORD Hosts to send: depart me to(wards) you
10 “Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
for who? to despise to/for day small and to rejoice and to see: see [obj] [the] stone [the] tin in/on/with hand Zerubbabel seven these eye LORD they(masc.) to rove in/on/with all [the] land: country/planet
11 Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
and to answer and to say to(wards) him what? two [the] olive [the] these upon right [the] lampstand and upon left her
12 Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
and to answer second and to say to(wards) him what? two ear [the] olive which in/on/with hand: to two pipe [the] gold [the] to empty from upon them [the] gold
13 Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
and to say to(wards) me to/for to say not to know what? these and to say not lord my
14 Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”
and to say these two son: descendant/people [the] oil [the] to stand: stand upon lord all [the] land: country/planet

< Zakariya 4 >