< Zakariya 4 >

1 Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
And he returned the angel who was speaking with me and he roused me like a person who he is roused from sleep his.
2 Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
And he said to me what? [are] you seeing (and I said *Q(K)*) I see - and there! a lampstand of gold all of it and a bowl [is] on top its and seven lamps its [are] on it seven and seven pipes [belong] to the lamps which [are] on top its.
3 Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
And two olive trees [were] at it one from [the] right [side] of the bowl and one at left [side] its.
4 Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
And I answered and I said to the angel who was speaking with me saying what? [are] these O lord my.
5 Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
And he answered the angel who was speaking with me and he said to me ¿ not do you know what? they [are] these and I said no O lord my.
6 Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And he answered and he said to me saying this [is] [the] word of Yahweh to Zerubbabel saying not by strength and not by power that except by spirit my he says Yahweh of hosts.
7 “Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
Who? [are] you O mountain great before Zerubbabel level ground and he will bring forth the stone top shouting grace grace to it.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
And it came [the] word of Yahweh to me saying.
9 “Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
[the] hands of Zerubbabel they have founded the house this and hands his they will finish [it] and you will know that Yahweh of hosts he has sent me to you.
10 “Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
For who? has he despised a day of small [things] and they will rejoice and they will see the stone tin in [the] hand of Zerubbabel seven these [the] eyes of Yahweh they [are] roving about in all the earth.
11 Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
And I answered and I said to him what? [are] [the] two the olive trees these at [the] right [side] of the lampstand and at left [side] its.
12 Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
And I answered a second [time] and I said to him what? [are] [the] two [the] clusters of the olive trees which [are] at [the] hand of [the] two [the] pipes of gold which are pouring out from on them the gold.
13 Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
And he said to me saying ¿ not do you know what? [are] these and I said no O lord my.
14 Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”
And he said these [are] [the] two [the] sons of the fresh oil who stand at [the] lord of all the earth.

< Zakariya 4 >