< Zakariya 4 >

1 Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
And the angel that talked with me came again, and awaked me, as a man that is wakened out of his sleep,
2 Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
and said to me, What seest thou? And I said, I have looked, and behold, a chandelier all of gold, with a bowl upon the top of it, and its seven lamps upon it, and seven pipes to the seven lamps which are upon the top of it;
3 Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
and two olive-trees by it, one upon the right side of the bowl, and the other upon the left side of it.
4 Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
And I spake, and said to the angel that talked with me, What mean these, my lord?
5 Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
Then the angel who talked with me answered and said to me, Knowest thou not what these mean? And I said, No, my lord.
6 Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Then he answered and spake to me, saying, This is the word of Jehovah to Zerubbabel, saying: — Not by might, nor by power, But by my spirit, Saith Jehovah of hosts.
7 “Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
What art thou, O great mountain? Before Zerubbabel thou shalt become a plain! And he shall bring forth the corner-stone amid shoutings, [[The people crying, ]] “Grace, grace be to it!”
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
Moreover, the word of Jehovah came to me, saying:
9 “Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
The hands of Zerubbabel have laid the foundation of this house, and his hands shall finish it. And thou shalt know that Jehovah of hosts hath sent me to you.
10 “Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
For who hath despised the day of small things? With joy shall the plummet be seen in the hand of Zerubbabel by those seven; they are the eyes of Jehovah, which run to and fro through the whole earth.
11 Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
Then I spake and said to him, What mean these two olive-trees, upon the right side of the chandelier and upon the left side thereof?
12 Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
And I spake the second time, and said to him, What mean these two olive-branches, which are by the side of the two golden tubes which empty the golden oil out of themselves?
13 Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
And he answered me and said, Knowest thou not what these mean? And I said, No, my lord.
14 Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”
And he said, These are the two anointed ones that stand before the Lord of all the earth.

< Zakariya 4 >