< Zakariya 4 >
1 Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
And the angel that spoke with me came back again, and waked me up, as a man that is wakened up out of his sleep;
2 Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
And he said unto me, What art thou seeing? And I said, I have looked, and behold, there is a candlestick all of gold, with a bowl upon its top, and its seven lamps are thereupon, and seven pipes to the seven lamps, which are upon its top:
3 Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
And two olive-trees are by it, one upon the right side of the bowl, and the other upon the left side thereof.
4 Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
And I commenced and said unto the angel that spoke with me, saying, What are these, my lord?
5 Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
Then the angel that spoke with me answered and said unto me, Knowest thou not what these are? And I said, No, my lord.
6 Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Then answered he and spoke unto me, saying, This is the word of the Lord unto Zerubbabel, saying, Not by might, nor by power, but by my spirit, saith the Lord of hosts.
7 “Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
Who art thou, O great mountain? before Zerubbabel thou wilt become a plain: and he shall bring forth the headstone with shoutings of, Grace, grace unto it.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
And the word of the Lord came unto me, saying,
9 “Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
The hands of Zerubbabel have laid the foundation of this house, and his hands shall complete it: and thou shalt know that the Lord of hosts hath sent me unto you.
10 “Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
For whoever even despised the day of [its] small beginning: yet will they rejoice when they see the plummet in the hand of Zerubbabel, with those seven; they are the eyes of the Lord, which hold a survey through all the earth.
11 Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
And I began, and said unto him, What are these two olive-trees upon the right side of the candle-stick and upon its left?
12 Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
And I began a second time, and said unto him, What are these two olive-branches, which are close by the two golden pipes which empty out of themselves the gold-colored oil?
13 Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
And he said to me as followeth, Knowest thou not what these things are? And I said, No, my lord.
14 Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”
Then said he, These are the two sons of the clear oil, that stand by the Lord of the whole earth.