< Zakariya 4 >

1 Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
Engelen, som talte med mig, vakte mig saa atter, som man vækker et Menneske af hans Søvn,
2 Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
og spurgte mig: »Hvad skuer du?« Jeg svarede: »Jeg skuer, og se, der er en Lysestage, helt og holdent af Guld, og et Oliekar ovenpaa og syv Lamper og syv Rør til Lamperne,
3 Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
desuden to Olietræer ved Siden af den, et til højre, et andet til venstre for Oliekarret.«
4 Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
Og jeg spurgte Engelen, som talte med mig: »Hvad betyder disse Ting, Herre?«
5 Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
Han svarede: »Ved du ikke, hvad de betyder?« Jeg sagde: »Nej, Herre!«
6 Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Da svarede han og sagde til mig: Dette er HERRENS Ord til Zerubbabel: Ikke ved Magt og ikke ved Styrke, men ved min Aand, siger Hærskarers HERRE.
7 “Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
Hvem er du, du store Bjerg? For Zerubbabel skal du blive Slette! Han skal hente Topstenen, medens der raabes: »Naade, Naade være med den!«
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
Og HERRENS Ord kom til mig saaledes:
9 “Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
Zerubbabels Hænder har lagt Grunden til dette Hus, hans Hænder skal ogsaa fuldende det; og du skal kende, at Hærskarers HERRE har sendt mig til eder.
10 “Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
Thi den, der lod haant om de ringe Begyndelsers Dag, skal glæde sig, naar han ser Blystenen i Zerubbabels Haand. Hine syv er HERRENS Øjne, som søger ud over hele Jorden.
11 Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
Derpaa spurgte jeg ham: »Hvad betyder de to Olietræer der til højre og venstre for Lysestagen?«
12 Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
Og videre spurgte jeg: »Hvad betyder de to Oliegrene ved Siden af de to Guldrør, som leder den gyldne Olie ned derfra?«
13 Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
Han svarede: »Ved du ikke, hvad de betyder?« Jeg sagde: »Nej, Herre!«
14 Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”
Saa sagde han: »Det er de to med Olie salvede, som staar for al Jordens Herre.«

< Zakariya 4 >