< Zakariya 4 >
1 Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
Potom navrátil se anděl, kterýž mluvil se mnou, a zbudil mne jako muže, kterýž zbuzen bývá ze sna svého.
2 Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
I řekl mi: Co vidíš? Jemuž jsem řekl: Vidím, že aj, svícen zlatý všecken, a olejný dčbán na vrchu jeho, a sedm lamp jeho na něm, a sedm nálevek k těm sedmi lampám, kteréž jsou na vrchu jeho.
3 Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
A dvě olivy při něm, jedna po pravé straně dčbánu olejného, a druhá po levé straně jeho.
4 Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
Tehdy odpověděl jsem a řekl jsem andělu tomu, kterýž mluvil ke mně, řka: Co ty věci jsou, pane můj?
5 Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
A odpovídaje anděl, kterýž mluvil se mnou, řekl mi: Což nevíš, co ty věci jsou? I řekl jsem: Nevím, pane můj.
6 Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Tedy odpovídaje, mluvil ke mně, řka: Toto jest slovo Hospodinovo k Zorobábelovi, řkoucí: Ne silou, ani mocí, ale Duchem mým, praví Hospodin zástupů.
7 “Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
Co jsi ty, ó horo veliká, před Zorobábelem? Rovina. Nebo doloží nejvyšší kámen s hlučným prokřikováním: Milost, milost jemu.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
I stalo se slovo Hospodinovo ke mně, řkoucí:
9 “Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
Ruce Zorobábelovy založily dům tento, a ruce jeho dokonají. I zvíš, že Hospodin zástupů poslal mne k vám.
10 “Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
Nebo kdož by pohrdal dnem malých začátků, poněvadž se veselí, hledíce na ten kámen, totiž na závaží v ruce Zorobábelově, těch sedm očí Hospodinových, procházejících všecku zemi?
11 Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
Tedy odpovídaje jemu, řekl jsem? Co ty dvě olivy po pravé straně toho svícnu, i po levé straně jeho?
12 Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
Opět odpovídaje jemu, řekl jsem: Co ty dvě olivky, kteréž jsou mezi dvěma trubicemi zlatými, kteréž vylévají z sebe zlato?
13 Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
I mluvil ke mně, řka: Víš-liž, co ty věci jsou? I řekl jsem: Nevím, pane můj.
14 Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”
Tedy řekl: To jsou ty dvě olivy, kteréž jsou u Panovníka vší země.