< Zakariya 3 >

1 Sa’an nan ya nuna mini Yoshuwa babban firist a tsaye a gaban mala’ikan Ubangiji, Shaiɗan kuma yana tsaye a damansa don yă tuhume shi.
Pokazal mi je Ješúa, vélikega duhovnika, stati pred Gospodovim angelom in Satana, stoječega na njegovi desnici, da se mu upira.
2 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ubangiji ya tsawata maka, Shaiɗan! Ubangiji wanda ya zaɓi Urushalima, ya tsawata maka! Ashe, mutumin nan ba shi ne sandar da take ƙonewa da aka ciro daga cikin wuta ba?”
Gospod je rekel Satanu: » Gospod te oštej, oh Satan. Celó Gospod, ki je izbral Jeruzalem, naj te ošteje. Mar ni to ogorek, potegnjen iz ognja?«
3 Yanzu an sa wa Yoshuwa tufafi masu dauda sa’ad da yake tsaye a gaban mala’ikan.
Torej Ješúa je bil oblečen v umazane obleke in stal pred angelom.
4 Mala’ikan ya ce wa waɗanda suke tsaye a gabansa, “Ku cire masa tufafinsa masu dauda.” Sai ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ɗauke zunubanka, zan sa maka tufafi masu tsada.”
Odgovoril je in spregovoril tistim, ki so stali pred njim, rekoč: »Odvzemite umazane obleke z njega.« Rekel mu je: »Glej, tvoji krivičnosti sem velel, da gre od tebe in oblekel te bom z zamenjavo oblačil.«
5 Sai na ce, “Sa masa rawani mai tsabta a kansa.” Aka sa masa rawani mai tsabta a kansa aka kuma sa masa tufafi yayinda mala’ikan Ubangiji yake tsaye a wurin.
Rekel sem: »Naj na njegovo glavo postavijo lep turban.« Tako so na njegovo glavo postavili lep turban in ga oblekli z oblekami. In Gospodov angel je stal poleg.
6 Mala’ikan Ubangiji ya yi wa Yoshuwa wannan gargaɗi.
Gospodov angel je izpričal Ješúu, rekoč:
7 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘In za ka yi tafiya a hanyoyina ka kuma kiyaye abubuwan da nake so, za ka zama shugaban haikalina, ka kuma lura da ɗakunan shari’ata, zan kuma ba ka wuri cikin waɗannan da suke tsaye a nan.
»Tako govori Gospod nad bojevniki: ›Če se boš ravnal po mojih poteh in če se boš držal moje zadolžitve, potem boš sodil tudi mojo hišo in se boš držal mojih dvorov in dal ti bom prostore za hojo med tistimi, ki stojijo poleg.
8 “‘Ka saurara, ya babban firist Yoshuwa, kai da abokanka da suke zaune a gabanka, ku da kuke alamun abubuwan da za su zo. Zan kawo bawana, wanda yake Reshe.
Poslušaj sedaj, oh Ješúa, véliki duhovnik, ti in tvoji tovariši, ki sedijo pred teboj, kajti oni so ljudje čudenja. Kajti, glej, privedel bom svojega služabnika MLADIKO.
9 Dubi dutsen da na ajiye a gaban Yoshuwa! Akwai idanu bakwai a kan wannan dutse guda, zan kuma yi rubutu a kansa,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘zan kuma kawar da zunubin ƙasan nan a rana ɗaya.
Kajti poglej, kamen, ki sem ga položil pred Ješúa. Na enem kamnu bo sedem oči. Glej, vrezal bom graviranje le-tega, « govori Gospod nad bojevniki »in krivičnost te dežele bom odstranil v enem dnevu.
10 “‘A wannan rana kowannenku zai gayyaci maƙwabcinsa yă zauna a ƙarƙashin itacen inabi da kuma na ɓaure,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
Na ta dan, « govori Gospod nad bojevniki, »boste vabili vsakdo svojega soseda pod trto in pod figovo drevo.«

< Zakariya 3 >