< Zakariya 3 >

1 Sa’an nan ya nuna mini Yoshuwa babban firist a tsaye a gaban mala’ikan Ubangiji, Shaiɗan kuma yana tsaye a damansa don yă tuhume shi.
Un viņš man rādīja augsto priesteri Jozua, stāvam Tā Kunga eņģeļa priekšā. Un sātans stāvēja viņam pa labo roku, viņu apsūdzēt.
2 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ubangiji ya tsawata maka, Shaiɗan! Ubangiji wanda ya zaɓi Urushalima, ya tsawata maka! Ashe, mutumin nan ba shi ne sandar da take ƙonewa da aka ciro daga cikin wuta ba?”
Bet Tas Kungs sacīja uz sātanu: lai Tas Kungs tevi rāj, sātan: lai tevi rāj Tas Kungs, kas Jeruzālemi izredzējis! Vai šī nav pagale, no uguns izrauta?
3 Yanzu an sa wa Yoshuwa tufafi masu dauda sa’ad da yake tsaye a gaban mala’ikan.
Un Jozuas bija apģērbts netīrās drēbēs, kad viņš stāvēja tā eņģeļa priekšā.
4 Mala’ikan ya ce wa waɗanda suke tsaye a gabansa, “Ku cire masa tufafinsa masu dauda.” Sai ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ɗauke zunubanka, zan sa maka tufafi masu tsada.”
Tad viņš (tas eņģelis) atbildēja un runāja uz tiem, kas viņa priekšā stāvēja, un sacīja: atņemiet tam tās netīrās drēbes. Un viņš uz to sacīja: redzi, tavu noziegumu es tev esmu atņēmis, un tevi apģērbšu ar svētku drēbēm.
5 Sai na ce, “Sa masa rawani mai tsabta a kansa.” Aka sa masa rawani mai tsabta a kansa aka kuma sa masa tufafi yayinda mala’ikan Ubangiji yake tsaye a wurin.
Un es sacīju: lai liek tīru cepuri viņam galvā. Un tie tam lika tīru cepuri galvā un tam apvilka drēbes, un Tā Kunga eņģelis stāvēja tur klāt.
6 Mala’ikan Ubangiji ya yi wa Yoshuwa wannan gargaɗi.
Tad Tā Kunga eņģelis Jozuam apliecināja un sacīja:
7 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘In za ka yi tafiya a hanyoyina ka kuma kiyaye abubuwan da nake so, za ka zama shugaban haikalina, ka kuma lura da ɗakunan shari’ata, zan kuma ba ka wuri cikin waɗannan da suke tsaye a nan.
Tā saka Tas Kungs Cebaot: ja tu staigāsi Manos ceļos un sargāsi Manu likumu, tad tev arī Manu namu būs tiesāt un arī Manus pagalmus sargāt, un Es tev došu pieiešanu to starpā, kas te stāv.
8 “‘Ka saurara, ya babban firist Yoshuwa, kai da abokanka da suke zaune a gabanka, ku da kuke alamun abubuwan da za su zo. Zan kawo bawana, wanda yake Reshe.
Klausies nu jel, Jozua, augstais priesteri, tu un tavi draugi, kas tavā priekšā, jo tie ir par brīnuma zīmi. Jo redzi, Es likšu nākt Savam kalpam Cemak (Atvasei).
9 Dubi dutsen da na ajiye a gaban Yoshuwa! Akwai idanu bakwai a kan wannan dutse guda, zan kuma yi rubutu a kansa,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘zan kuma kawar da zunubin ƙasan nan a rana ɗaya.
Jo redzi to akmeni, ko Es Jozuas priekšā esmu nolicis! Uz to vienu akmeni (skatās) septiņas acis. Redzi, Es ierakstīšu viņa rakstu, saka Tas Kungs Cebaot, un atņemšu šās zemes noziegumu vienā dienā.
10 “‘A wannan rana kowannenku zai gayyaci maƙwabcinsa yă zauna a ƙarƙashin itacen inabi da kuma na ɓaure,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
Tai dienā, saka Tas Kungs Cebaot, jūs aicināsiet cits citu apakš vīna koka un apakš vīģes koka.

< Zakariya 3 >