< Zakariya 3 >

1 Sa’an nan ya nuna mini Yoshuwa babban firist a tsaye a gaban mala’ikan Ubangiji, Shaiɗan kuma yana tsaye a damansa don yă tuhume shi.
Puis [l'Eternel] me fit voir Jéhosuah, le grand Sacrificateur, se tenant debout devant l'Ange de l'Eternel; et Satan qui se tenait debout à sa droite, pour le contrarier.
2 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ubangiji ya tsawata maka, Shaiɗan! Ubangiji wanda ya zaɓi Urushalima, ya tsawata maka! Ashe, mutumin nan ba shi ne sandar da take ƙonewa da aka ciro daga cikin wuta ba?”
Et l'Eternel dit à Satan: Que l'Eternel te tance [rudement], ô Satan! Que l'Eternel, dis-je, qui a élu Jérusalem, te tance [rudement!] N'est-ce pas ici ce tison [qui a été] retiré du feu?
3 Yanzu an sa wa Yoshuwa tufafi masu dauda sa’ad da yake tsaye a gaban mala’ikan.
Or Jéhosuah était vêtu de vêtements sales, et il se tenait debout devant l'Ange.
4 Mala’ikan ya ce wa waɗanda suke tsaye a gabansa, “Ku cire masa tufafinsa masu dauda.” Sai ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ɗauke zunubanka, zan sa maka tufafi masu tsada.”
Et [l’Ange] prit la parole, et dit à ceux qui étaient debout devant lui: Otez de dessus lui ces vêtements sales. Et il dit à [Jéhosuah]: Regarde, j'ai fait passer de dessus toi ton iniquité, et je t'ai vêtu de nouveaux vêtements.
5 Sai na ce, “Sa masa rawani mai tsabta a kansa.” Aka sa masa rawani mai tsabta a kansa aka kuma sa masa tufafi yayinda mala’ikan Ubangiji yake tsaye a wurin.
Et je dis: Qu'on lui mette une tiare nette sur sa tête; et on lui mit sur la tête une tiare nette; puis on le vêtit de vêtements, et l'Ange de l'Eternel était présent.
6 Mala’ikan Ubangiji ya yi wa Yoshuwa wannan gargaɗi.
Alors l'Ange de l'Eternel protesta à Jéhosuah, en disant:
7 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘In za ka yi tafiya a hanyoyina ka kuma kiyaye abubuwan da nake so, za ka zama shugaban haikalina, ka kuma lura da ɗakunan shari’ata, zan kuma ba ka wuri cikin waɗannan da suke tsaye a nan.
Ainsi a dit l'Eternel des armées: Si tu marches dans mes voies, et que tu observes ce que je veux qui soit observé, tu auras la juridiction de ma maison, et tu garderas mes parvis, et je ferai que tu marcheras parmi ces assistants.
8 “‘Ka saurara, ya babban firist Yoshuwa, kai da abokanka da suke zaune a gabanka, ku da kuke alamun abubuwan da za su zo. Zan kawo bawana, wanda yake Reshe.
Ecoute maintenant, Jéhosuah, grand Sacrificateur, toi, et tes compagnons qui sont assis devant toi, parce que ce sont des gens qu'on tient pour des monstres, certainement voici, je m'en vais faire venir Germe, mon serviteur.
9 Dubi dutsen da na ajiye a gaban Yoshuwa! Akwai idanu bakwai a kan wannan dutse guda, zan kuma yi rubutu a kansa,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘zan kuma kawar da zunubin ƙasan nan a rana ɗaya.
Car voici, [quant à] la pierre que j'ai mise devant Jéhosuah, sur [cette] pierre, qui n'est qu'une, il y a sept yeux. Voici, je m'en vais graver sa gravure, dit l'Eternel des armées, et j'ôterai en un jour l'iniquité de ce pays.
10 “‘A wannan rana kowannenku zai gayyaci maƙwabcinsa yă zauna a ƙarƙashin itacen inabi da kuma na ɓaure,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
En ce jour-là, dit l'Eternel des armées, chacun de vous appellera son prochain sous la vigne et sous le figuier.

< Zakariya 3 >